< 1 Chronicles 19 >

1 And it came to pass after this, that Nachash the king of the children of 'Ammon died, and his son became king in his stead.
Ana nan, sai Nahash sarkin Ammonawa ya mutu, sai ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 And David said, I will show kindness unto Chanun the son of Nachash, because his father showed kindness unto me. And David sent messengers to comfort him concerning his father. And the servants of David came unto the land of the children of 'Ammon to Chanun, to comfort him.
Dawuda ya yi tunani, “Zan nuna jinƙai ga Hanun ɗan Nahash, domin mahaifinsa ya nuna alheri gare ni.” Saboda haka Dawuda ya aika da tawaga don yă yi wa Hanun ta’aziyya game da mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka iso wurin Hanun a ƙasar Ammonawa don su ta’azantar da shi,
3 And the princes of the children of 'Ammon said unto Chanun, Doth David honor thy father in thy eyes, that he hath sent comforters unto thee? are not his servants come unto thee in order to search out, and to overthrow, and to spy out the land?
sai manyan Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aika mutanen nan wurinka su ta’azantar da kai? Ba mutanensa sun zo ne su bincika su kuma leƙi ƙasar su tumɓuke ta ba?”
4 Chanun thereupon took David's servants, and shaved them, and cut off their garments in the middle as far as the hip-bone, and sent them away.
Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda, ya yi musu aski, ya yayyanka rigunansu a daidai ɗuwawunsu, sa’an nan ya sallame su.
5 And some people went and told David concerning these men. And he sent [persons] to meet them: because the men were greatly ashamed; and the king said, Tarry at Jericho until your beard be grown, and then return.
Da wani ya zo ya faɗa wa Dawuda game da mutanen, sai ya aiki’yan aika su sadu da su, gama an ƙasƙantar da su ainun. Sarki ya ce, “Ku zauna a Yeriko har sai gemunku sun yi girma, sa’an nan ku dawo.”
6 And when the children of 'Ammon saw that they were become in bad odor with David, Chanun and the children of 'Ammon sent a thousand talents of silver to hire for themselves from Mesopotamia, and from Syria-ma'achah, and from Zobah, chariots and horsemen.
Sa’ad da Ammonawa suka gane cewa sun zama abin wurin a kafan hancin Dawuda, Hanun da Ammonawa suka aika da talenti dubu na azurfa don su yi haya da kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi daga Aram-Naharayim, Aram Ma’aka da Zoba.
7 And they hired for themselves thirty and two thousand [warriors in] chariots, and the king of Ma'achah and his people: and they came and encamped before Medeba. And the children of 'Ammon gathered themselves together out of their cities, and came to the battle.
Suka yi hayar kekunan yaƙi da mahayan kekunan yaƙi dubu talatin da biyu, da kuma sarkin Ma’aka tare da mayaƙansa, waɗanda suka zo suka kafa sansani kusa da Medeba, yayinda Ammonawa suka tattaru daga garuruwansu suka fita yaƙi.
8 And when David heard of it, he sent Joab, and all the army [and] the mighty men.
Da jin haka, Dawuda ya aiki Yowab tare da dukan mayaƙa masu yaƙi.
9 And the children of 'Ammon came out, and put themselves in battle array at the entrance of the city: and the kings that were come were by themselves in the field.
Ammonawa suka fito suka ja dāgā a ƙofar birninsu, yayinda sarakunan da suka zo, su kansu suka ware suna a fili.
10 When now Joab saw that the front of battle was against him before and behind, he made a selection from all the chosen men of Israel, and arrayed himself against the Syrians.
Yowab ya ga cewa akwai dāgā a gabansa da bayansa; sai ya zaɓi waɗansu mayaƙa mafi kyau a Isra’ila ya sa su a kan Arameyawa.
11 And the rest of the people he delivered into the hand of Abshai his brother, and they arrayed themselves against the children of 'Ammon.
Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin kulawar Abishai ɗan’uwansa, aka sa a kan Ammonawa.
12 And he said, If the Syrians be too strong for me, then shalt thou bring me help; but if the children of 'Ammon be too strong for thee, then will I help thee.
Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ni ƙarfi, sai ka kawo mini ɗauke da ni; amma in Ammonawa sun fi ka ƙarfi, sai in kawo maka ɗauke.
13 Be strong, and let us strengthen ourselves in behalf of our people, and in behalf of the cities of our God, and may the Lord do that which seemeth good in his eyes.
Ka yi ƙarfin hali bari mu yi yaƙi da jaruntaka saboda mutanenmu da biranen Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da ya ga ya yi masa kyau.”
14 And Joab drew nigh and the people that were with him in front of the Syrians unto the battle, and they fled from before him.
Sai Yowab da ƙungiyoyin mayaƙan da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Arameyawa, Arameyawan kuwa suka gudu a gabansa.
15 And when the children of 'Ammon saw that the Syrians were fled, then did they also fly before Abshai his brother, and entered into the city. And Joab went back to Jerusalem.
Sa’ad da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka guda a gaban ɗan’uwansa Abishai suka shiga cikin birni. Sai Yowab ya koma Urushalima.
16 And when the Syrians saw that they were smitten before Israel, they sent messengers, and brought out the Syrians that were beyond the river: and Shophach the captain of the army of Hadar'ezer went before them.
Bayan Arameyawa suka ga cewa Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka aiki’yan aika suka sa aka kawo Arameyawan da suke hayen Kogi waɗanda Shobak shugaban mayaƙan Hadadezer yake shugabanta.
17 And when it was told to David, he gathered all Israel together, and passed over the Jordan, and came up with them, and arrayed himself against them. So when David had arrayed himself against the Syrians [for] battle, they fought with him.
Sa’ad da aka faɗa wa Dawuda wannan, sai tattara dukan Isra’ila ya haye Urdun; ya tafi wurinsu ya kuwa ja dāgā ɗaura da su. Dawuda ya ja dāgārsa don yă sadu da Arameyawa a yaƙi, su kuwa suka yi yaƙi da shi.
18 And the Syrians fled from before Israel: and David slew of the Syrians [the men of] seven thousand chariots, and forty thousand men on foot, and Shophach the captain of the army he put to death.
Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, mutanen Dawuda kuwa suka kashe masu hawan keken yaƙinsu dubu bakwai da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya kuma kashe Shobak shugaban mayaƙansu.
19 And when the vassals of Hadar'ezer saw that they were smitten before Israel, they made peace with David, and served him: and the Syrians would not help the children of 'Ammon any more.
Da abokan tarayyar Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka nemi salama da Dawuda suka kuma zama bayinsa. Saboda haka Arameyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.

< 1 Chronicles 19 >