< 2 Chronicles 1 >

1 And Solomon the son of David strengthened himself in his kingdom, and the Lord his God was with him, and caused him to become exceedingly great.
Solomon ɗan Dawuda ya kafa kansa sosai a bisa masarautarsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi ya kuma sa ya zama mai girma sosai.
2 Then said Solomon unto all Israel, to the captains of the thousands and of the hundreds, and to the judges, and to every prince in all Israel, the chiefs of the family divisions [that they should go with him].
Sai Solomon ya yi magana ga dukan Isra’ila, ga shugabannin mayaƙa dubu-dubu da shugabannin mayaƙa ɗari-ɗari, ga alƙalai da kuma ga dukan shugabanni a Isra’ila, kawunan iyalai,
3 Thereupon went Solomon, and all the assembly with him, to the high-place that was at Gib'on; for there was the tabernacle of the congregation of God, which Moses the servant of the Lord had made in the wilderness.
Solomon tare da dukan taron suka tafi masujadan kan tudu a Gibeyon, gama Tentin Sujadar Allah yana can, wanda Musa bawan Ubangiji ya yi a hamada.
4 Nevertheless the ark of God had David brought up from Kiryath-ye'arim to [the place which] David had prepared for it; for he had pitched a tent for it at Jerusalem.
Dawuda ya riga ya haura da akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim zuwa inda ya shirya dominsa, domin yă kafa masa tenti a Urushalima.
5 But the copper altar, which Bezalel the son of Uri, the son of Chur, had made, he placed before the tabernacle of the Lord: and Solomon and the assembly sought for it.
Amma bagaden tagullar da Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, ya yi a Gibeyon a gaba tabanakul na Ubangiji; saboda haka Solomon da taron suka neme nufin Ubangiji a can.
6 And Solomon sacrificed there on the copper altar before the Lord, which was at the tabernacle of the congregation, and offered upon it a thousand burnt-offerings.
Solomon ya haura zuwa bagaden tagulla a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada, ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa dubbai a kansa.
7 In that night did God appear unto Solomon, and said unto him, Ask what I shall give thee.
A wannan dare Allah ya bayyana ga Solomon, ya ce masa, “Roƙi duk abin da kake so in ba ka.”
8 And Solomon said unto God, Thou hast shown unto David my father great kindness, and hast made me king in his stead.
Solomon ya amsa wa Allah, “Ka nuna alheri mai girma ga Dawuda mahaifina ka kuma naɗa ni sarki a matsayinsa.
9 Now, O Lord God, let thy word unto David my father be verified; for thou hast made me king over a people as numerous as the dust of the earth.
To, yanzu, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi ga mahaifina Dawuda yă tabbata, gama ka naɗa ni sarki a bisa mutanen da suka wuce ƙirge kamar ƙurar ƙasa.
10 Give me now wisdom and knowledge, that I may go out and come in before this people; for who could [otherwise] judge this thy great people?
Ka ba ni hikima da sani, don in iya jagorance wannan mutane, gama wa zai iya shugabance wannan jama’arka mai girma?”
11 And God said unto Solomon, Whereas this hath been in thy heart, and thou hast not asked riches, wealth, or honor, nor the life of thy enemies, and hast not even asked long life; but hast asked for thyself wisdom and knowledge, that thou mayest judge my people, over whom I have made thee king:
Allah ya ce wa Solomon, “Da yake wannan ne sha’awar zuciyarka, ba ka kuwa nemi wadata, arziki ko girma ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, da yake kuma ba ka nemi tsawon rai ba, amma ka nemi hikima da sani don ka shugabanci jama’ata wadda na naɗa ka sarki,
12 [Therefore] are the wisdom and the knowledge granted unto thee; and riches, and wealth, and honor, will I give thee, such as no kings that have been before thee have had, and the like of which after thee none shall have.
saboda haka za a ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka wadata, arziki da girma, waɗanda babu wani sarki kafin kai da ya taɓa kasance da su kuma babu wani a bayanka da zai kasance da su.”
13 Then came Solomon from the high-place that was at Gib'on to Jerusalem, from before the tabernacle of the congregation, and reigned over Israel.
Sa’an nan Solomon ya tafi Urushalima daga masujadar kan tudu a Gibeyon, da kuma daga gaban Tentin Sujada. Ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila.
14 And Solomon brought together chariots and horsemen; and he had a thousand and four hundred chariots, and twelve thousand horsemen, and he placed them in the chariot-cities, and with the king at Jerusalem.
Solomon ya tara kekunan yaƙi da dawakai, ya kasance da kekunan yaƙi dubu da ɗari huɗu da kuma dawakai dubu goma sha biyu, waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi, da kuma tare da shi a Urushalima.
15 And the king rendered the silver and gold at Jerusalem like stones, and cedar-trees he rendered as the sycamore-trees that are in the lowlands for abundance.
Sarki ya sa azurfa da zinariya suka zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
16 And Solomon had his horses brought out of Egypt; a company of the king's merchants bought a quantity at a price.
Aka shigo da dawakan Solomon daga Masar da kuma daga Kuye’yan kasuwan fada suka saye su daga Kuye.
17 And they brought up, and fetched out of Egypt a chariot for six hundred shekels of silver, and a horse for a hundred and fifty; and so for all the kings of the Hittites, and for the kings of Syria, did they bring them out by their means.
Suka shigo da kekunan yaƙi daga Masar a kan shekel ɗari shida-shida na azurfa, doki kuma a kan shekel ɗari da hamsin-hamsin. Suka kuma riƙa fitar da su ƙasashen waje zuwa dukan sarakunan Hittiyawa da na Arameyawa.

< 2 Chronicles 1 >