< Psalms 80 >

1 To the chief Musician upon Shoshannim-eduth, A Psalm of Asaph. Give ear, O Shepherd of Israel, thou that leadest Joseph like a flock; thou that dwellest [between] the cherubims, shine forth.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
2 Before Ephraim and Benjamin and Manasseh stir up thy strength, and come [and] save us.
a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
3 Turn us again, O God, and cause thy face to shine; and we shall be saved.
Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
4 O LORD God of hosts, how long wilt thou be angry against the prayer of thy people?
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
5 Thou feedest them with the bread of tears; and givest them tears to drink in great measure.
Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
6 Thou makest us a strife unto our neighbours: and our enemies laugh among themselves.
Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
7 Turn us again, O God of hosts, and cause thy face to shine; and we shall be saved.
Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
8 Thou hast brought a vine out of Egypt: thou hast cast out the heathen, and planted it.
Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
9 Thou preparedst [room] before it, and didst cause it to take deep root, and it filled the land.
Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
10 The hills were covered with the shadow of it, and the boughs thereof [were like] the goodly cedars.
Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
11 She sent out her boughs unto the sea, and her branches unto the river.
Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
12 Why hast thou [then] broken down her hedges, so that all they which pass by the way do pluck her?
Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
13 The boar out of the wood doth waste it, and the wild beast of the field doth devour it.
Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
14 Return, we beseech thee, O God of hosts: look down from heaven, and behold, and visit this vine;
Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
15 And the vineyard which thy right hand hath planted, and the branch [that] thou madest strong for thyself.
saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
16 [It is] burned with fire, [it is] cut down: they perish at the rebuke of thy countenance.
An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
17 Let thy hand be upon the man of thy right hand, upon the son of man [whom] thou madest strong for thyself.
Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
18 So will not we go back from thee: quicken us, and we will call upon thy name.
Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
19 Turn us again, O LORD God of hosts, cause thy face to shine; and we shall be saved.
Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.

< Psalms 80 >