< Psalms 71 >

1 In thee, O LORD, do I put my trust: let me never be put to confusion.
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2 Deliver me in thy righteousness, and cause me to escape: incline thine ear unto me, and save me.
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3 Be thou my strong habitation, whereunto I may continually resort: thou hast given commandment to save me; for thou [art] my rock and my fortress.
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
4 Deliver me, O my God, out of the hand of the wicked, out of the hand of the unrighteous and cruel man.
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
5 For thou [art] my hope, O Lord GOD: [thou art] my trust from my youth.
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
6 By thee have I been holden up from the womb: thou art he that took me out of my mother’s bowels: my praise [shall be] continually of thee.
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
7 I am as a wonder unto many; but thou [art] my strong refuge.
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
8 Let my mouth be filled [with] thy praise [and with] thy honour all the day.
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
9 Cast me not off in the time of old age; forsake me not when my strength faileth.
Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
10 For mine enemies speak against me; and they that lay wait for my soul take counsel together,
Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
11 Saying, God hath forsaken him: persecute and take him; for [there is] none to deliver [him].
Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
12 O God, be not far from me: O my God, make haste for my help.
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
13 Let them be confounded [and] consumed that are adversaries to my soul; let them be covered [with] reproach and dishonour that seek my hurt.
Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
14 But I will hope continually, and will yet praise thee more and more.
Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
15 My mouth shall shew forth thy righteousness [and] thy salvation all the day; for I know not the numbers [thereof].
Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
16 I will go in the strength of the Lord GOD: I will make mention of thy righteousness, [even] of thine only.
Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
17 O God, thou hast taught me from my youth: and hitherto have I declared thy wondrous works.
Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
18 Now also when I am old and grayheaded, O God, forsake me not; until I have shewed thy strength unto [this] generation, [and] thy power to every one [that] is to come.
Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
19 Thy righteousness also, O God, [is] very high, who hast done great things: O God, who [is] like unto thee!
Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
20 [Thou], which hast shewed me great and sore troubles, shalt quicken me again, and shalt bring me up again from the depths of the earth.
Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
21 Thou shalt increase my greatness, and comfort me on every side.
Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
22 I will also praise thee with the psaltery, [even] thy truth, O my God: unto thee will I sing with the harp, O thou Holy One of Israel.
Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
23 My lips shall greatly rejoice when I sing unto thee; and my soul, which thou hast redeemed.
Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
24 My tongue also shall talk of thy righteousness all the day long: for they are confounded, for they are brought unto shame, that seek my hurt.
Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.

< Psalms 71 >