< Psalms 74 >

1 Maschil of Asaph. O God, why hast thou cast [us] off for ever? [why] doth thine anger smoke against the sheep of thy pasture?
Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
2 Remember thy congregation, [which] thou hast purchased of old; the rod of thine inheritance, [which] thou hast redeemed; this mount Zion, wherein thou hast dwelt.
Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
3 Lift up thy feet unto the perpetual desolations; [even] all [that] the enemy hath done wickedly in the sanctuary.
Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
4 Thine enemies roar in the midst of thy congregations; they set up their ensigns [for] signs.
Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
5 [A man] was famous according as he had lifted up axes upon the thick trees.
Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
6 But now they break down the carved work thereof at once with axes and hammers.
Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
7 They have cast fire into thy sanctuary, they have defiled [by casting down] the dwelling place of thy name to the ground.
Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
8 They said in their hearts, Let us destroy them together: they have burned up all the synagogues of God in the land.
Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
9 We see not our signs: [there is] no more any prophet: neither [is there] among us any that knoweth how long.
Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
10 O God, how long shall the adversary reproach? shall the enemy blaspheme thy name for ever?
Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
11 Why withdrawest thou thy hand, even thy right hand? pluck [it] out of thy bosom.
Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
12 For God [is] my King of old, working salvation in the midst of the earth.
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
13 Thou didst divide the sea by thy strength: thou brakest the heads of the dragons in the waters.
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
14 Thou brakest the heads of leviathan in pieces, [and] gavest him [to be] meat to the people inhabiting the wilderness.
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
15 Thou didst cleave the fountain and the flood: thou driedst up mighty rivers.
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
16 The day [is] thine, the night also [is] thine: thou hast prepared the light and the sun.
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
17 Thou hast set all the borders of the earth: thou hast made summer and winter.
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
18 Remember this, [that] the enemy hath reproached, O LORD, and [that] the foolish people have blasphemed thy name.
Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
19 O deliver not the soul of thy turtledove unto the multitude [of the wicked: ] forget not the congregation of thy poor for ever.
Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
20 Have respect unto the covenant: for the dark places of the earth are full of the habitations of cruelty.
Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
21 O let not the oppressed return ashamed: let the poor and needy praise thy name.
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
22 Arise, O God, plead thine own cause: remember how the foolish man reproacheth thee daily.
Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
23 Forget not the voice of thine enemies: the tumult of those that rise up against thee increaseth continually.
Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.

< Psalms 74 >