< Job 12 >

1 And Job answered and said,
Sai Ayuba ya amsa,
2 No doubt but ye [are] the people, and wisdom shall die with you.
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 But I have understanding as well as you; I [am] not inferior to you: yea, who knoweth not such things as these?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 I am [as] one mocked of his neighbour, who calleth upon God, and he answereth him: the just upright [man is] laughed to scorn.
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 He that is ready to slip with [his] feet [is as] a lamp despised in the thought of him that is at ease.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 The tabernacles of robbers prosper, and they that provoke God are secure; into whose hand God bringeth [abundantly].
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 But ask now the beasts, and they shall teach thee; and the fowls of the air, and they shall tell thee:
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 Or speak to the earth, and it shall teach thee: and the fishes of the sea shall declare unto thee.
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Who knoweth not in all these that the hand of the LORD hath wrought this?
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 In whose hand [is] the soul of every living thing, and the breath of all mankind.
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 Doth not the ear try words? and the mouth taste his meat?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 With the ancient [is] wisdom; and in length of days understanding.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 With him [is] wisdom and strength, he hath counsel and understanding.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 Behold, he breaketh down, and it cannot be built again: he shutteth up a man, and there can be no opening.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Behold, he withholdeth the waters, and they dry up: also he sendeth them out, and they overturn the earth.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 With him [is] strength and wisdom: the deceived and the deceiver [are] his.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 He leadeth counsellors away spoiled, and maketh the judges fools.
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 He looseth the bond of kings, and girdeth their loins with a girdle.
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 He leadeth princes away spoiled, and overthroweth the mighty.
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 He removeth away the speech of the trusty, and taketh away the understanding of the aged.
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 He poureth contempt upon princes, and weakeneth the strength of the mighty.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 He discovereth deep things out of darkness, and bringeth out to light the shadow of death.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 He increaseth the nations, and destroyeth them: he enlargeth the nations, and straiteneth them [again].
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 He taketh away the heart of the chief of the people of the earth, and causeth them to wander in a wilderness [where there is] no way.
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 They grope in the dark without light, and he maketh them to stagger like [a] drunken [man].
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.

< Job 12 >