< Job 11 >

1 Then answered Zophar the Naamathite, and said,
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Should not the multitude of words be answered? and should a man full of talk be justified?
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 Should thy lies make men hold their peace? and when thou mockest, shall no man make thee ashamed?
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 For thou hast said, My doctrine [is] pure, and I am clean in thine eyes.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 But oh that God would speak, and open his lips against thee;
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 And that he would shew thee the secrets of wisdom, that [they are] double to that which is! Know therefore that God exacteth of thee [less] than thine iniquity [deserveth].
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 Canst thou by searching find out God? canst thou find out the Almighty unto perfection?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 [It is] as high as heaven; what canst thou do? deeper than hell; what canst thou know? (Sheol h7585)
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
9 The measure thereof [is] longer than the earth, and broader than the sea.
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 If he cut off, and shut up, or gather together, then who can hinder him?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 For he knoweth vain men: he seeth wickedness also; will he not then consider [it]?
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 For vain man would be wise, though man be born [like] a wild ass’s colt.
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 If thou prepare thine heart, and stretch out thine hands toward him;
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 If iniquity [be] in thine hand, put it far away, and let not wickedness dwell in thy tabernacles.
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 For then shalt thou lift up thy face without spot; yea, thou shalt be stedfast, and shalt not fear:
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 Because thou shalt forget [thy] misery, [and] remember [it] as waters [that] pass away:
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 And [thine] age shall be clearer than the noonday; thou shalt shine forth, thou shalt be as the morning.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 And thou shalt be secure, because there is hope; yea, thou shalt dig [about thee, and] thou shalt take thy rest in safety.
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 Also thou shalt lie down, and none shall make [thee] afraid; yea, many shall make suit unto thee.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 But the eyes of the wicked shall fail, and they shall not escape, and their hope [shall be as] the giving up of the ghost.
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”

< Job 11 >