< Psalms 44 >
1 We have heard with our ears, O God, our fathers have told us, what work you did in their days, in the times of old.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 How you did drive out the heathen with your hand, and planted them; how you did afflict the people, and cast them out.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 For they got not the land in possession by their own sword, neither did their own arm save them: but your right hand, and your arm, and the light of your countenance, because you had a favor to them.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 You are my King, O God: command deliverances for Jacob.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Through you will we push down our enemies: through your name will we tread them under that rise up against us.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 For I will not trust in my bow, neither shall my sword save me.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 But you have saved us from our enemies, and have put them to shame that hated us.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 In God we boast all the day long, and praise your name for ever. (Selah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 But you have cast off, and put us to shame; and go not forth with our armies.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 You make us to turn back from the enemy: and they which hate us spoil for themselves.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 You have given us like sheep appointed for meat; and have scattered us among the heathen.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 You sell your people for nothing, and do not increase your wealth by their price.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 You make us a reproach to our neighbors, a scorn and a derision to them that are round about us.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 You make us a byword among the heathen, a shaking of the head among the people.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 My confusion is continually before me, and the shame of my face has covered me,
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 For the voice of him that reproaches and blasphemes; by reason of the enemy and avenger.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 All this is come on us; yet have we not forgotten you, neither have we dealt falsely in your covenant.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Our heart is not turned back, neither have our steps declined from your way;
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 Though you have sore broken us in the place of dragons, and covered us with the shadow of death.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 If we have forgotten the name of our God, or stretched out our hands to a strange god;
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 Shall not God search this out? for he knows the secrets of the heart.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Yes, for your sake are we killed all the day long; we are counted as sheep for the slaughter.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Awake, why sleep you, O Lord? arise, cast us not off for ever.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Why hide you your face, and forget our affliction and our oppression?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 For our soul is bowed down to the dust: our belly sticks to the earth.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Arise for our help, and redeem us for your mercies’ sake.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.