< Revelation 18 >

1 After this I saw another angel descending from heaven. He had great power and the earth was lit up by his glory.
Bayan wadannan abubuwa sai na ga wani mala'ika yana saukowa daga sama. Yana da babban iko sosai, duniya kuwa ta haskaka da daukakarsa.
2 He shouted out in a powerful voice, “Babylon the great has collapsed into ruins! She has become a place where demons live, the refuge of every unclean spirit, and the roost of every unclean and detestable bird.
Ya yi kira da kakkarfar murya cewa, “Ta fadi, Babila mai girma ta fadi! Ta zama mazaunin aljannu, da matattarar kowanne kazamin ruhu da kuma mazaunin kowanne kazami da kyamataccen tsuntsu.
3 For all the nations have drunk the wine of her mad sexual immorality. The kings of the earth have committed adultery with her, and the traders of the earth have grown rich from her excessive sensuality.”
Gama dukan al'ummai sun sha ruwan innabin fasikancinta. Sarakunan duniya sun aikata fasikanci da ita. Attajiran duniya sun arzuta da ikon rayuwar annashuwarta.”
4 Then I heard another voice from heaven calling out, “My people, come out of her, so that you don't participate in her sinful ways, and so that you don't experience her plagues.
Sai na ji wata murya daga sama ta ce, “Ku fito daga cikinta, mutanena, domin kada kuyi zunubi irin na ta, domin kuma kada bala'inta ya auko maku.
5 Her sins have piled up all the way to heaven, and God is very much aware of her wickedness.
Zunubanta sun taru sun yi tsayi har sama. Allah kuma ya tuna da miyagun ayyukanta.
6 Give back to her what she gave; repay her double for what she did. In her own cup mix double the trouble she mixed for others.
Ku saka mata gwargwadon yadda ta saka wa wadansu, ku biya ta ninki biyu na abin da ta yi; a cikin kokon da ta dama, ku dama mata ninki biyu.
7 As much as she boasted about herself and indulged her lusts, give her back just as much anguish and sorrow. She told herself, ‘I reign as queen. I am no widow; I will never be in mourning.’
Kamar yadda ta daukaka kanta ta yi ta annashuwa, ku wahalsheta da azaba da bakin ciki haka. Domin ta ce a zuciyarta, 'Ina zaune kamar sarauniya; ni ba gwauruwa ba ce, kuma ba zan taba yin makoki ba,'
8 Because of this her plagues will come upon her in just one day: death, mourning, and famine. She will be completely destroyed by fire, for the Lord God who condemns her has great power.
Saboda haka a rana daya bala'inta zai auko mata; mutuwa, makoki da kuma yunwa. Wuta za ta kona ta kurmus, domin Ubangiji Allah mai iko ne, kuma shine mai hukuntata.”
9 The kings of the earth who had committed adultery with her and indulged their lusts with her will cry and mourn over her when they see the smoke of the fire that destroys her.
Sarakunan duniya da suka yi fasikanci, har suka baude tare da ita, za su yi kuka da kururuwa domin ta sa'adda suka ga hayakin kunarta.
10 Standing off at a distance because they are afraid they will suffer the same agony as her, they say, ‘Disaster, disaster has struck Babylon, the great city! In just one hour your sentence of doom was executed!’
Za su tsaya can nesa suna tsoron azabarta, suna cewa, “Kaito, kaiton babban birni, Babila, birni mai iko! Domin cikin sa'a guda hukuncinta ya zo.”
11 The traders of the earth cry and grieve over her, because nobody is buying their goods any more—
Manyan 'yan kasuwan duniya za su yi kuka da bakin ciki dominta, da shike ba wanda ke sayan kayanta kuma -
12 products made of gold, silver, gems and pearls; fine linen, purple cloth, silk, and scarlet material; all kinds of objects made of scented wood, or from ivory, or expensive woods, or bronze, iron, or marble;
kayan zinariya, azurfa, da duwatsun alfarma, da lu'u-lu'u, da lilin mai laushi, da hajja mai ruwan jar garura, da siliki, da jar alharini da itacen kamshi iri iri, da kayan da aka sassaka da itace mai tsada, da na tagulla, da na bakin karfe, da na dutse mai sheki,
13 shipments of cinnamon, spice, incense, myrrh, frankincense, wine, olive oil, fine flour and wheat, cattle and sheep, horses and wagons, and slaves and prisoners.
da kirfa, da kayan yaji, da turaren wuta, da mur da lubban, da ruwan innabi, da mai, da garin alkama, da alkama, da shanu, da tumaki, da dawakai, da kekunan doki, da bayi, da rayukan 'yan adam.
14 You've lost the sweet pleasures you loved so much; all your luxurious, glittering possessions are gone—you'll never get any of them back.
Amfanin da kika kwallafa rai da duk karfinki sun fice daga gareki. Duk annashuwarki da darajarki sun bace, ba za a kara samunsu ba kuma.
15 The traders who sold these things and became rich from trading with her will stand at a distance because they are afraid they will suffer the same agony as her. They will cry and grieve, saying,
Manyan 'yan kasuwa na wadannan kaya da suka azurta ta wurinta, za su tsaya can nesa da ita, sabili da tsoron azabarta, kuka da kururuwar bakin ciki.
16 ‘Disaster, disaster has hit the great city! She was clothed in fine linen and purple robes, and wore jewelry made of gold and gems and pearls.
Za su ce, “Kaito, kaito ga babban birni da take sanye da lilin mai laushi da tufafi masu jar garura da kuma jan alharini, da ta ci ado da kayan zinariya, da duwatsu masu daraja da lu'u-lu'u!
17 In just one hour all this wealth was destroyed!’ Every sea captain and everyone who travels by sea and every sailor and everyone who earns their living from the sea stood at a distance.
A cikin sa'a guda duk dukiyan nan ta lallace. Kowanne matukin jirgin ruwa, da fasinjoji, da masu tuki da duk wadanda suke samun biyan bukatun rayuwarsu daga ruwa, suka tsaya can nesa.
18 As they watched the smoke of the fire that destroys her, they shouted out, ‘What city could ever compare to this great city?’
Suka yi kuka sa'anda suka ga hayakin kunarta. Suka ce, “Wanne birni ne ya yi kama da babban birnin?”
19 They threw dust on their heads, shouting and crying and grieving, ‘Disaster, disaster has struck the great city that made every ship-owner rich because of her extravagance! In just one hour she was destroyed!’
Suka watsa kura a kawunansu, suka yi kuka da karfi, da kururuwa da bakin ciki, “Kaito, kaiton babban birnin nan inda duk masu jiragen ruwa suka azurta daga dukiyarta. Domin a sa'a guda an hallakar da ita.”
20 Celebrate what's happened to her, heaven and believers and apostles and prophets, for God has condemned her as she condemned you.”
“Ku yi murna a kanta, sama, ku masu ba da gaskiya, manzanni, da annabawa, domin Allah ya kawo hukuncinku a kanta!”
21 A powerful angel picked up a rock the size of a large millstone and threw it into the sea, saying, “With this kind of violence the great city of Babylon will be thrown down, and will never exist again.”
Wani kakkarfan mala'ika ya dauki wani dutse mai kama da dutsen nika, ya jefa shi cikin teku yana cewa, “Ta wannan hanya, Babila, babban birnin, za a jefar da ita kasa da karfi, ba za a kara ganinsa ba.
22 “Never again will anyone hear music in you: the sound of harps, singers, flutes, and trumpets. Never again will craftsmen of any trade work in you. Never again will the sound of a mill be heard in you.
Muryar masu kidar molaye, mawaka, masu busa sarewa, da na masu busa algaita, ba za a kara ji a cikinta ba. Babu wani mai kowanne irin sana'a da za a samu a cikinta. Ba za a kara jin karar nika a cikinta ba.
23 Never again will the light of a lamp shine in you. Never again will the voices of bridegroom and bride be heard in you. Your traders led the world. Through your witchcraft all the nations were deceived.
Hasken fitila ba za ya kara haskakawa a cikin ki ba. Ba za a kara jin muryoyin ango da na amarya a cikinki ba, domin attajiranki sune 'ya'yan masu mulki a duniya, kuma ta wurin sihirinki kika yaudari al'ummai.
24 In her the blood of prophets and believers was found, and of all those who have been killed on the earth.”
A cikinta aka sami jinin annabawa da na masu ba da gaskiya, da jinin duk wadanda aka kashe a duniya.”

< Revelation 18 >