< John 9 >

1 As Jesus was passing by, he saw a man born blind.
Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa.
2 His disciples asked him, “Rabbi, why was this man born blind? Was it him who sinned, or was it his parents?”
Sai almajiransa suka tambaye shi, “Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?”
3 Jesus replied, “It wasn't because the man or his parents sinned. But so that what God can do may be shown in his life,
Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa.
4 we have to keep on doing the work of the one who sent me as long as it is still daytime. The night is coming when no one can work.
Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki.
5 While I'm here in the world I am the light of the world.”
Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya.”
6 After he'd said this, Jesus spat on the ground and made some mud with the saliva which he put on the man's eyes.
Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
7 Then Jesus told him, “Go and wash in the Pool of Siloam” (which means “sent”). So the man went and washed, and when he went home he could see.
Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8 His neighbors and those who had known him as a beggar, asked, “Isn't this the man who used to sit and beg?”
Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
9 Some said he was, while others said “no, it's just someone who looks like him.” But the man kept saying, “It is me!”
Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
10 “So how is it you can see?” they asked him.
Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
11 He replied, “A man called Jesus made some mud and put it on my eyes and told me, ‘Go and wash yourself in the Pool of Siloam.’ So I went and washed, and now I can see.”
Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
12 “Where is he?” they asked. “I don't know,” he replied.
Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
13 They took the man who had been blind to the Pharisees.
Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
14 Now it was the Sabbath when Jesus had made the mud and opened the blind man's eyes.
A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
15 So the Pharisees also asked him how he could see. He told them, “He put mud on my eyes, and I washed, and now I can see.”
Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, “Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani.”
16 Some of the Pharisees said, “The man who did this can't be from God because he doesn't keep the Sabbath.” But others wondered, “How could a sinner do such miracles?” So they were divided in their opinion.
Wadansu daga cikin farisawa suka ce, “Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. “Wadansu suka ce, “Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?” Sai rabuwa ta shiga tsakanin su.
17 So they went on questioning the man. “What's your opinion about him, then, since it's your eyes he opened,” they asked. “He's surely a prophet,” the man replied.
Sai suka tambayi makahon kuma, “Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?” Makahon ya ce, “shi annabi ne.”
18 The Jewish leaders still refused to believe that the man who had been blind could now see until they had called in the man's parents.
Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
19 They asked them, “Is this your son whom you say was born blind? So how is it that now he can see?”
Su ka tambayi iyayen, “Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?”
20 His parents answered, “We know this is our son who was born blind.
Sai iyayen suka amsa masu, “Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi.
21 But we've no idea how he can see now, or who healed him. Why don't you ask him, he's old enough. He can speak for himself.”
Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa.”
22 The reason his parents said this was because they were afraid of what the Jewish leaders would do. The Jewish leaders had already announced that anyone who declared that Jesus was the Messiah would be thrown out of the synagogue.
Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a.
23 That was why his parents said, “Ask him, he's old enough.”
Domin wannan ne, iyayensa suka ce, “Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
24 Once more they called in the man who had been blind, and told him, “Give God the glory! We know this man is a sinner.”
Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, “Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne.”
25 The man replied, “Whether he's a sinner or not, I don't know. All I know is that I was blind and now I can see.”
Sai wannan mutum ya amsa, “Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani.”
26 Then they asked him, “What did he do to you? How did he open your eyes?”
Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
27 The man replied, “I already told you. Weren't you listening? Why do you want to hear it again? You don't want to become his disciples too, do you?”
Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
28 They shouted abuse at him, and said, “You're that man's disciple.
Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
29 We're disciples of Moses. We know that God spoke to Moses, but as for this person, we don't even know where he comes from.”
Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
30 The man answered, “That's incredible! You don't know where he comes from but he opened my eyes.
Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
31 We know that God doesn't listen to sinners, but he does listen to anyone who worships him and does what he wants.
Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
32 Never before in the whole of history has anyone heard of a man born blind being healed. (aiōn g165)
Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. (aiōn g165)
33 If this man weren't from God, he could do nothing.”
In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
34 “You were born totally sinful, and yet you're trying to lecture us,” they replied. And they threw him out of the synagogue.
Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
35 When Jesus heard that they had thrown him out, he went and found the man, and asked him, “Do you trust in the Son of man?”
Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
36 The man replied, “Tell me who he is, sir, so I can put my trust in him.”
Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
37 “You've already seen him. He's the one speaking with you now!” Jesus told him.
Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
38 “I trust you, Lord!” he said, and he kneeled in worship before Jesus.
Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
39 Then Jesus told him, “I've come into the world to bring judgment so that those who are blind may see, and those who see will become blind.”
Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
40 Some Pharisees who were there with Jesus asked him, “We're not blind too, are we?”
Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, “Muma makafi ne?”
41 Jesus answered, “If you were blind, you wouldn't be guilty. But now that you say you see, your guilt remains.”
Yesu ya ce masu, “Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.

< John 9 >