< Luke 1 >

1 As you know, many others have attempted to put down in writing the things that have been fulfilled that involve us.
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 They based their accounts on evidence from the earliest eyewitnesses and ministers of the Word,
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 and so I also decided that since I have followed these things very carefully from the beginning, it would be a good idea to write out an accurate account of all that happened.
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 I have done this dear Theophilus so you can be certain that what you were taught is completely reliable.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 During the time when Herod was king of Judea, there was a priest called Zechariah, who came from the Abijah priestly division. He was married to Elizabeth, who was also descended from Aaron the priest.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 They both did what was right before God, being careful to follow all the Lord's commandments and regulations.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 They had no children because Elizabeth wasn't able to have any, and they were both growing old.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 While Zechariah was serving as a priest before God, on behalf of his priestly division,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 he was chosen by lot according to priestly custom to enter the Temple of the Lord and burn incense.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 During the time of offering incense a large crowd of people were praying outside.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 An angel of the Lord appeared to Zechariah, standing to the right of the altar of incense.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 When Zechariah saw the angel, he was startled and became terrified.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 But the angel told him, “Don't be afraid, Zechariah. Your prayer has been heard, and your wife Elizabeth will bear you a son, and you shall call him John.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 He will bring you joy and gladness, and many will celebrate his birth.
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 He will be great in the sight of the Lord. He will refuse to drink wine or other alcoholic drink. He will be filled with the Holy Spirit even before he's born.
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 He will turn many Israelites back to the Lord their God.
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 He will go ahead of the Lord in the spirit and power of Elijah, to turn the fathers back to thinking about their children, and to turn those who are rebellious back to a right understanding—to prepare a people ready for the Lord.”
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 “How can I be sure about this?” Zechariah asked the angel. “I'm an old man, and my wife is getting old too.”
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 “I am Gabriel,” the angel replied. “I stand in God's presence, and I was sent to speak to you and give you this good news.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 But since you didn't believe what I told you, you'll become dumb, unable to speak, until the appointed time when my words come true.”
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 Outside the people were waiting for Zechariah, wondering why he was taking so long in the Temple.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 When eventually he came out, he wasn't able to speak to them. They realized he'd seen a vision in the Temple, for though he could make gestures, he was completely dumb.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 After he'd finished his time of service, he went back home.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 Some time later his wife Elizabeth became pregnant. She stayed at home for five months.
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 “The Lord has done this for me,” she said, “now that he's taken away my disgrace in the eyes of others.”
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 In the sixth month of her pregnancy God sent the angel Gabriel to a young girl called Mary who lived in the town of Nazareth in Galilee.
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 She was engaged to a man named Joseph.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 The angel greeted her. “You are very privileged,” he told her. “The Lord is with you.”
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 Mary was very puzzled at what he said, and wondered what this greeting meant.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 “Don't worry, Mary,” the angel went on, “for God has shown his graciousness to you.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 You will become pregnant and give birth to a son. You shall call him Jesus.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 He will be very great, and he will be called the Son of the Most High. The Lord God will give him the throne of David his father,
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 and he will reign over the house of Jacob forever. His kingdom will never come to an end.” (aiōn g165)
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
34 “How is this possible?” Mary asked. “I'm still a virgin.”
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 He replied, “The Holy Spirit will come upon you, and the power of the Most High will cover you. The baby who is to be born is holy, and will be called the Son of God.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 And Elizabeth, your relative, even she is pregnant in her old age. The woman that people said couldn't have children is already six months pregnant.
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 Nothing is impossible for God.”
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 “Here I am, ready to be the Lord's servant,” said Mary. “May it happen to me just as you said.” Then the angel left her.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 A little while later, Mary got herself ready and hurried up into the hills of Judea, to the town where
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 Zechariah's house was. She called out to Elizabeth as she went in.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 As soon as Elizabeth heard Mary's voice, the baby jumped for joy inside her. Elizabeth was filled with the Holy Spirit,
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 and cried out in a loud voice, “How blessed you are among women, and how blessed will be the child born to you!
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 Why am I so honored that the mother of my Lord should visit me?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 As soon as I heard you call out in greeting, my baby jumped for joy inside me.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 How fortunate you are, because you are convinced that the Lord will do what he has promised you!”
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 Mary replied, “How I praise the Lord!
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 I am so happy with God my Savior,
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 because he decided that I, his servant, was worthy of his consideration, despite my humble background. From now on every generation will say I was blessed.
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 God Almighty has done great things for me; his name is holy.
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 His mercy lasts for generation after generation to those who respect him.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 With his power he has broken to pieces those who arrogantly think they're so clever.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 He tears the powerful down from their thrones, and elevates those who are humble.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 He fills the hungry with good things to eat, and he sends the rich away empty-handed.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 He has helped his servant Israel, remembering him in mercy,
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 just as he promised our fathers, to Abraham and his descendants for ever.” (aiōn g165)
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
56 Mary stayed with her for three months and then returned home.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 The time came for Elizabeth to have her baby and she gave birth to a son.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 Her neighbors and relatives heard how the Lord had showed her great kindness, and they celebrated together with her.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 Eight days later they came to circumcise the boy. They planned to call him Zechariah after his father.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 “No,” Elizabeth said. “He shall be called John.”
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 “But there's nobody among your relatives who has this name,” they told her.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 Through gestures they asked Zechariah, the boy's father, what he wanted to call his son.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 Zechariah motioned for something to write on. To everyone's surprise he wrote, “His name is John.”
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 Immediately he could speak again, and he started praising God.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 All those living nearby were in awe at what had happened, and the news spread throughout the hill country of Judea.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 Everyone who heard the news wondered what it meant. “What will the little boy grow up to be?” they asked, for it was clear he was very special to God.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 Zechariah, his father, filled with the Holy Spirit, spoke this prophecy:
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 “The Lord, the God of Israel, he is wonderful, for he has come to his people and set them free.
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 He has given us a great Savior from the line of his servant David,
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 as he promised through his holy prophets long ago. (aiōn g165)
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
71 He promised to save us from our enemies, from those who hate us.
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 He was merciful to our fathers, remembering his holy agreement—
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the promise that he made to our father Abraham.
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 He gives us freedom from fear and rescues us from our enemies,
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 so we can serve him by doing what is good and right for our whole lives.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 Even though you are only a small child, you will be called the prophet of the Most High, for you will go ahead of the Lord to prepare his way,
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 providing knowledge of salvation to his people through the forgiveness of their sins.
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 Through God's caring kindness to us, heaven's dawn will break upon us
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 to shine on those who live in darkness and under the shadow of death, and to guide us along the path of peace.”
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 The boy John grew and became spiritually strong. He lived in the desert until the time came for his public ministry to Israel.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.

< Luke 1 >