< Jeremiah 47 >

1 The word of the Lord that came to Jeremias the prophet against the people of Palestine, before Pharao took Gaza.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Filistiyawa kafin Fir’auna ya yaƙi Gaza.
2 Thus saith the Lord: Behold there come up waters out of the north, and they shall be as an overflowing torrent, and they shall cover the land, and all that is therein, the city and the inhabitants thereof: then the men shall cry, and all the inhabitants of the land shall howl,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dubi yadda ruwaye suna tasowa a arewa; za su zama kogi mai rigyawa. Za su malala a ƙasa da kuma a kan kome da yake cikinta, garuruwa da waɗanda suke zaune a cikinsu. Mutane za su yi kuka; dukan mazaunan ƙasar za su yi kururuwa
3 At the noise of the marching of arms, and of his soldiers, at the rushing of his chariots, and the multitude of his wheels. The fathers have not looked back to the children, for feebleness of hands,
da jin motsin takawar kofatan dawakai, da jin surutun kekunan yaƙin abokin gāba da motsin ƙafafunsu. Ubanni ba za su juye don su taimaki’ya’yansu ba; hannuwansu za su yi laƙwas.
4 Because of the coming of the day, in which all the Philistines shall be laid waste, and Tyre and Sidon shall be destroyed, with all the rest of their helpers. For the Lord hath wasted the Philistines, the remnant of the isle of Cappadocia.
Gama rana ta zo da za a hallaka Filistiyawa a kuma datse dukan waɗanda suka ragu waɗanda za su iya taimakon Taya da Sidon. Ubangiji yana gab da hallaka Filistiyawa, raguwa daga bakin tekun Kaftor.
5 Baldness is come upon Gaza: Ascalon hath held her peace with the remnant of their valley: how long shalt thou cut thyself?
Gaza za tă aske kanta cikin baƙin ciki; Ashkelon zai yi shiru. Ya raguwar da suke zama a fili, har yaushe za ku tsattsage kanku?
6 O thou sword of the Lord, how long wilt thou not be quiet? Go into thy scabbard, rest, and be still.
“Za ku yi kuka kuna cewa, ‘Wayyo, takobin Ubangiji sai yaushe za ka huta? Ka koma kubenka; ka huta, ka yi shiru.’
7 How shall it be quiet, when the Lord hath given it a charge against Ascalon, and against the countries thereof by the sea side, and there hath made an appointment for it?
Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”

< Jeremiah 47 >