< Jeremiah 46 >

1 The word of the Lord that came to Jeremias the prophet against the Gentiles,
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
2 Against Egypt, against the army of Pharao Nechao king of Egypt, which was by the river Euphrates in Charcamis, whom Nabuchodonosor the king of Babylon defeated, in the fourth year of Joakim the son of Josias king of Juda.
Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
3 Prepare ye the shield and buckler, and go forth to battle.
“Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
4 Harness the horses, and get up, ye horsemen: stand forth with helmets, furbish the spears, put on coats of mail.
Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
5 What then? I have seen them dismayed, and turning their backs, their valiant ones slain: they fled apace, and they looked not back: terror was round about, saith the Lord.
Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
6 Let not the swift flee away, nor the strong think to escape: they are overthrown, and fallen down, towards the north by the river Euphrates.
“Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
7 Who is this that cometh up as a flood: and his streams swell like those of rivers?
“Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
8 Egypt riseth up like a flood, and the waves thereof shall be moved as rivers, and he shall say: I will go up and will cover the earth: I will destroy the city, and its inhabitants.
Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
9 Get ye up on horses, and glory in chariots, and let the valiant men come forth, the Ethiopians, and the Libyans that hold the shield, and the Lydians that take, and shoot arrows.
Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
10 For this is the day of the Lord the God of hosts, a day of vengeance, that he may revenge himself of his enemies: the sword shall devour, and shall be filled, and shall be drunk with their blood: for there is a sacrifice of the Lord God of hosts in the north country, by the river Euphrates.
Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
11 Go up into Galaad, and take balm, O virgin daughter of Egypt: in vain dost thou multiply medicines, there shall be no cure for thee.
“Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
12 The nations have heard of thy disgrace, and thy howling hath filled the land: for the strong hath stumbled against the strong, and both are fallen together.
Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
13 The word that the Lord spoke to Jeremias the prophet, how Nabuchodonosor king of Babylon should come and strike the land of Egypt:
Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
14 Declare ye to Egypt, and publish it in Magdal, and let it be known in Memphis, and in Taphnis: say ye: Stand up, and prepare thyself: for the sword shall devour all round about thee.
“Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
15 Why are thy valiant men come to nothing? they stood not: because the Lord hath overthrown them.
Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
16 He hath multiplied them that fall, and one hath fallen upon another, and they shall say: Arise, and let us return to our own people, and to the land our nativity, from the sword of the dove.
Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
17 Call ye the name of Pharao king Egypt, a tumult time hath brought.
A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
18 As I live, (saith the King, whose name is the Lord of hosts, ) as Thabor is among the mountains, and as Carmel by the sea, so shall he come.
“Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
19 Furnish thyself to go into captivity, thou daughter inhabitant of Egypt: for Memphis shall be made desolate, and shall be forsaken and uninhabited.
Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
20 Egypt is like a fair and beautiful heifer: there shall come from the north one that shall goad her.
“Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
21 Her hirelings also that lived in the midst of her, like fatted calves are turned back, and are fled away together, and they could not stand, for the day of their slaughter is come upon them, the time of their visitation.
Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
22 Her voice shall sound like brass, for they shall hasten with an army, and with axes they shall come against her, as hewers of wood.
Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
23 They have cut down her forest, saith the Lord, which cannot be counted: they are multiplied above locusts, and are without number.
Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
24 The daughter of Egypt is confounded, and delivered into the hand of the people of the north.
Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
25 The Lord of hosts the God of Israel hath said: Behold I will visit upon the tumult of Alexandria, and upon Pharao, and upon Egypt, and upon her gods, and upon her kings, and upon Pharao, upon them that trust in him.
Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
26 And I will deliver them into the hand of them that seek their lives, into the hand of Nabuchodonosor king of Babylon, and into the hand of his servants: and afterwards it shall be inhabited, as in the days of old, saith the Lord.
Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
27 And thou my servant Jacob, fear not and be not thou dismayed, O Israel: for behold I will save thee from afar off, and thy seed out of the land of thy captivity: and Jacob shall return and be at rest, and prosper: and there shall be none to terrify him.
“Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
28 And thou, my servant Jacob, fear not, saith the Lord: because I am with thee, for I will consume all the nations to which I have cast thee out: but thee I will not consume, but I will correct thee in judgment, neither will I spare thee as if thou wert innocent.
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”

< Jeremiah 46 >