< Esther 4 >

1 Now when Mordecai saw what was done, pulling off his robe, he put on haircloth, with dust on his head, and went out into the middle of the town, crying out with a loud and bitter cry.
Sa’ad da Mordekai ya sami labari game da dukan abin da aka yi, sai ya yayyage rigunansa, ya sanya tsummokin makoki, ya zuba toka a kā, ya kuma shiga ciki birni yana kuka mai zafi da ƙarfi.
2 And he came even before the king's doorway; for no one might come inside the king's door clothed in haircloth.
Amma ya kai bakin ƙofar sarki ne kawai, gama ba a yarda wani sanye da tsummokin makoki yă shiga cikin birni ba.
3 And in every part of the kingdom, wherever the king's word and his order came, there was great sorrow among the Jews, and weeping and crying and going without food; and numbers of them were stretched on the earth covered with dust and haircloth.
Aka yi makoki sosai da azumi, da kuka mai zafi a cikin Yahudawa a kowane lardin da aka kai doka da kuma umarnin sarki. Mutane da yawa suka kwanta a cikin tsummokin makoki da kuma toka.
4 And Esther's women and her servants came and gave her word of it. Then great was the grief of the queen: and she sent robes for Mordecai, so that his clothing of haircloth might be taken off; but he would not have them.
Sa’ad da bayi da bābānnin Esta suka zo suka faɗa mata game da Mordekai, sai ta damu ƙwarai. Ta aika masa da riguna domin yă sa a maimakon tsummokin makoki, amma ya ƙi.
5 Then Esther sent for Hathach, one of the king's unsexed servants whom he had given her for waiting on her, and she gave him orders to go to Mordecai and see what this was and why it was.
Sai Esta ta kira Hatak, ɗaya daga cikin bābānnin sarkin da aka ba shi aikin lura da ita, ta umarce shi yă yi tambaya me ke damun Mordekai da kuma me ya jawo haka.
6 So Hathach went out and saw Mordecai in the open square of the town before the king's doorway.
Saboda haka Hatak ya tafi wurin Mordekai a dandalin birni, a gaban ƙofar sarki.
7 And Mordecai gave him an account of what had taken place, and of the amount of money which Haman had said he would put into the king's store for the destruction of the Jews.
Mordekai ya faɗa masa duk abin da ya faru da shi, haɗe da yawan kuɗin da Haman ya yi alkawari zai zuba a ma’ajin fada don a hallaka Yahudawa.
8 And he gave him the copy of the order which had been given out in Shushan for their destruction, ordering him to let Esther see it, and to make it clear to her; and to say to her that she was to go in to the king, requesting his mercy, and making prayer for her people.
Ya kuma ba shi kofi na rubutaccen doka na kakkaɓe su, wanda aka wallafa a Shusha don yă nuna wa Esta, yă bayyana mata. Mordekai ya faɗa wa Hatak yă iza ta tă tafi gaban sarki domin tă yi roƙo don jinƙai, tă kuma roƙe shi saboda mutanenta.
9 And Hathach came back and gave Esther an account of what Mordecai had said.
Hatak ya koma ya ba wa Esta rahoton abin da Mordekai ya faɗa.
10 Then Esther sent Hathach to say to Mordecai:
Sa’an nan Esta ta umarce Hatak yă ce wa Mordekai,
11 It is common knowledge among all the king's servants and the people of every part of the kingdom, that if anyone, man or woman, comes to the king in his inner room without being sent for, there is only one law for him, that he is to be put to death; only those to whom the king's rod of gold is stretched out may keep their lives: but I have not been sent for to come before the king these thirty days.
“Dukan hafsoshin sarki da mutanen lardunan sarki sun san cewa duk wanda ya tafi wurin sarki a shirayi na ciki, mace ko namiji, ba tare da an kira shi ba, doka ɗaya ce take kan mutum, wato, kisa. Abu guda kawai da ya sha bamban shi ne sai wanda sarki ya miƙa wa sandan sarauta na zinariya don yă rayu. Kwana talatin ke nan ba a kira ni in tafi wurin sarki ba.”
12 And they said these words to Mordecai.
Sa’ad da aka kai wa Mordekai rahoton maganan Esta,
13 Then Mordecai sent this answer back to Esther: Do not have the idea that you in the king's house will be safe from the fate of all the Jews.
sai ya mayar da wannan amsa wa Esta cewa, “Kada ki yi tsammani cewa don kina a cikin gidan sarki, ke kaɗai cikin dukan Yahudawa za ki tsira.
14 If at this time you say nothing, then help and salvation will come to the Jews from some other place, but you and your father's family will come to destruction: and who is to say that you have not come to the kingdom even for such a time as this?
Gama in kin yi shiru a wannan lokaci, taimako da ceto zai zo daga wani wuri saboda Yahudawa, amma ke da gidanki za ku hallaka. Wa ya san ko saboda irin wannan lokaci ne kika sami wannan muƙami?”
15 Then Esther sent them back to Mordecai with this answer:
Sai Esta ta aika da wannan amsa ga Mordekai cewa,
16 Go, get together all the Jews who are present in Shushan, and go without food for me, taking no food or drink night or day for three days: and I and my women will do the same; and so I will go in to the king, which is against the law: and if death is to be my fate, then let it come.
“Ka tafi, ka tattara dukan Yahudawan da suke Shusha, ku yi azumi saboda ni. Kada ku ci ko ku sha, dare da rana har kwana uku. Ni kuwa da bayina za mu yi azumi yadda kuke yi. Idan aka yi haka, zan tafi wurin sarki, ko da yake wannan karya doka ce. Idan na hallaka, to, na hallaka.”
17 So Mordecai went away and did everything as Esther had said.
Saboda haka, Mordekai ya tafi, ya aikata dukan umarnan Esta.

< Esther 4 >