< Esther 3 >
1 After these things, by the order of the king, Haman, the son of Hammedatha the Agagite, was lifted up and given a position of honour and a higher place than all the other captains who were with him.
Bayan waɗannan al’amura, sai Sarki Zerzes ya girmama Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, ya ɗaukaka shi, ya kuma ba shi matsayi mafi girma fiye da na dukan sauran hakiman.
2 And all the king's servants who were in the king's house went down to the earth before Haman and gave him honour: for so the king had given orders. But Mordecai did not go down before him or give him honour.
Dukan masu hidimar da suke a ƙofar sarki suka riƙa durƙusa suna ba wa Haman girma, gama sarki ya ba da umarni a yi masa haka. Amma Mordekai bai durƙusa ya ba shi girma ba.
3 Then the king's servants who were in the king's house said to Mordecai, Why do you go against the king's order?
Sa’an nan masu hidimar da suke a ƙofar sarki suka tambaye Mordekai, “Me ya sa ba ka yin biyayya da umarnin sarki?”
4 Now when they had said this to him day after day and he gave no attention, they let Haman have news of it, to see if Mordecai's behaviour would be overlooked: for he had said to them that he was a Jew.
Kowace rana suna masa magana, amma ya ƙi yă yi. Saboda haka, suka faɗa wa Haman game da wannan don su ga ko za a jure da halin Mordekai, gama ya faɗa musu cewa shi mutumin Yahuda ne.
5 And when Haman saw that Mordecai did not go down before him and give him honour, Haman was full of wrath.
Sa’ad da Haman ya ga cewa Mordekai ba ya durƙusa ko yă girmama shi, sai ya fusata.
6 But it was not enough for him to make an attack on Mordecai only; for they had made clear to him who Mordecai's people were; so Haman made it his purpose to put an end to all the Jews, even Mordecai's people, through all the kingdom of Ahasuerus.
Da yake an faɗa masa asalin Mordekai, sai ya ga a kashe Mordekai kaɗai ba zai biya masa bukata ba. A maimakon haka, Haman ya nemi hanya a hallaka dukan mutanen Mordekai, wato, Yahudawa, a ko’ina a dukan masarautar Zerzes.
7 In the first month, the month Nisan, in the twelfth year of King Ahasuerus, from day to day and from month to month they went on looking for a sign given by Pur (that is chance) before Haman, till the sign came out for the thirteenth day of the twelfth month, the month Adar.
A shekara ta goma sha biyu ta Sarki Zerzes, a wata na farko, watan Nisan, sai suka jefa fur (wato, ƙuri’a) a gaban Haman don a zaɓi rana da watan da zai dace da ƙulle-ƙullen. Sai ƙuri’a ta fāɗa a kan wata na goma sha biyu, wato, watan Adar.
8 And Haman said to King Ahasuerus, There is a certain nation living here and there in small groups among the people in all the divisions of your kingdom; their laws are different from those of any other nation, and they do not keep the king's laws: for this reason it is not right for the king to let them be.
Sai Haman ya ce wa Sarki Zerzes, “Akwai waɗansu mutanen da suke a warwatse, sun kuma bazu a cikin mutane cikin dukan lardunan masarautarka, waɗanda al’adunsu sun yi dabam da na dukan sauran mutane. Mutanen nan ba sa biyayya da dokokin sarki; ba zai yi wa sarki kyau a jure su ba.
9 If it is the king's pleasure, let a statement ordering their destruction be put in writing: and I will give to those responsible for the king's business, ten thousand talents of silver for the king's store-house.
In ya gamshi sarki, bari a yi doka, don a hallaka su, zan kuma sa talenti dubu goma na azurfa a cikin ma’ajin fada saboda mutanen da suka aikata wannan sha’ani.”
10 And the king took his ring from his hand and gave it to Haman, the son of Hammedatha the Agagite, the hater of the Jews.
Saboda haka sarki ya zare zoben hatimi daga yatsarsa, ya ba wa Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, abokin gāban Yahudawa.
11 And the king said to Haman, The money is yours, and the people, to do with them whatever seems right to you.
Sarki ya ce wa Haman, “Ka riƙe kuɗin, ka kuma yi da mutanen yadda ka ga dama.”
12 Then on the thirteenth day of the first month, the king's scribes were sent for, and they put in writing Haman's orders to all the king's captains and the rulers of every division of his kingdom and the chiefs of every people: for every division of the kingdom in the writing commonly used there, and to every people in the language which was theirs; it was signed in the name of King Ahasuerus and stamped with the king's ring.
Sa’an nan aka kira magatakardun sarki a rana ta goma sha uku na wata na fari. Suka rubuta dukan umarnin Haman a irin rubutun kowane lardi, kuma cikin harshen kowane mutane, zuwa ga shugabannin mahukuntai na sarki, da gwamnonin larduna dabam-dabam, da kuma hakiman mutane dabam-dabam. Aka rubuta waɗannan a sunan Sarki Zerzes da kansa, aka kuma hatimce da zobensa.
13 And letters were sent by the runners into every division of the kingdom ordering the death and destruction of all Jews, young and old, little children and women, on the same day, even the thirteenth day of the twelfth month, the month Adar, and the taking of all their goods by force.
Aka aika’yan-kada-tă-kwana da saƙoni zuwa dukan lardunan sarki da umarni a hallaka, a karkashe, a kuma kawar da dukan Yahudawa, manya da ƙanana, mata da yara, a kuma washe kayayyakinsu.
14 A copy of the writing, to be made public in every part of the kingdom, was sent out to all the peoples, so that they might be ready when that day came.
Za a ba da kofin rubutun a matsayin doka a kowane lardi, a kuma sanar da mutanen kowace al’umma, domin su zauna da shiri don wannan rana.
15 The runners went out quickly by the king's order, and a public statement was made in Shushan: and the king and Haman took wine together: but the town of Shushan was troubled.
Bisa ga umarnin sarki, sai’yan-kada-tă-kwana, suka tafi da sauri. Aka ba da umarni a mazaunin masarauta da yake a Shusha. Sai Sarki da Haman suka zauna don su sha, amma birnin Shusha ya ruɗe.