< Acts 3 >

1 Now Peter and John were going up together into the temple at the hour of prayer, which was the ninth hour.
Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku.
2 And a certain man, lame from his mother’s womb, was carried along, whom they laid daily at that gate of the temple which is called Beautiful, that he might ask charity of those who were going into the temple.
Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin.
3 This man, seeing Peter and John about to go into the temple, asked charity.
Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.
4 But Peter, fixing his eyes on him with John, said: Look on us.
Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, ''Ka dube mu.''
5 And he gave heed to them, expecting to receive something from them.
Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su.
6 But Peter said: Silver and gold I have none: but what I have, this I give you. In the name of Jesus Christ the Nazarene, arise and walk.
Amma Bitrus ya ce, “Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya''
7 And he took him by his right hand and raised him up: and immediately his feet and ankles received strength.
Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi.
8 And leaping up, he stood and walked, and went with them into the temple, walking and leaping and praising God.
Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.
9 And all the people saw him walking and praising God;
Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah.
10 and they recognized him, that it was he that had sat for charity at the Beautiful gate of the temple. And they were filled with wonder and amazement at what had happened to him.
Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.
11 And while he was holding to Peter and John, all the people ran together to them in the porch called Solomon’s, greatly astonished.
Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai.
12 But when Peter saw it, he answered the people: Men of Israel, why are you astonished at this? or, why do you look so earnestly on us, as if by our own power or godliness we had caused this man to walk?
Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, “Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?” Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?
13 The God of Abraham, and of Isaac, and of Jacob, the God of our fathers, has glorified his Son Jesus, whom you delivered up, and whom you rejected in the presence of Pilate, when he was determined to release him.
Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi.
14 But you rejected the Holy and Just One, and demanded that a murderer should be given to you;
Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.
15 and you slew the Author of life, whom God has raised from the dead, of which we are witnesses.
Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari.
16 And his name, by faith in his name, has made this man strong whom you see and know; even the faith which is by him, has given him this entire soundness in the presence of you all.
Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.
17 And now, brethren, I know that through ignorance you did this, as did also your rulers.
Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi.
18 But the things which God foretold by the mouth of all his prophets, that the Christ should suffer, he has thus fulfilled.
Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.
19 Repent, therefore, and turn, in order that your sins may be blotted out, so that seasons of refreshing may come from the presence of the Lord,
Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo;
20 and that he may send Jesus Christ, who was destined for you;
domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.
21 whom heaven must retain, till the time for restoring all things that God has spoken by the mouth of his holy prophets of ancient times. (aiōn g165)
Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. (aiōn g165)
22 For Moses said to the fathers, A prophet like me shall the Lord your God raise up for you from among your brethren; him shall you hear in all things that he shall say to you.
Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku.
23 And it shall come to pass, that every soul that will not hear that prophet, shall be destroyed from among the people.
Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'
24 And all the prophets, from Samuel and those that follow after, as many as have spoken, have also foretold these days.
I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki.
25 You are the sons of the prophets, and of the covenant that God made with our fathers, saying to Abraham, And in your offspring shall all the families of the earth be blessed.
Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.'
26 To you first, God, having raised up his Son Jesus, has sent him to bless you, in turning every one of you away from his iniquities.
Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa.”

< Acts 3 >