< Romans 1 >

1 Paul, a servant of Jesus Christ, a called apostle, set apart for the gospel of God,
Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah.
2 which he formerly promised through his prophets in the holy scriptures,
Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa.
3 concerning his Son Jesus Christ our Lord, who was born of the posterity of David according to the flesh,
Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.
4 but declared to be the Son of God with power, according to his holy spiritual nature, by his resurrection from the dead,
Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu.
5 through whom we have received grace and apostleship, in order to the obedience of faith among all nations, for the honor of his name,
Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa.
6 among whom are you also the called of Jesus Christ,
cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.
7 to all that are in Rome, beloved of God, called saints: Grace be to you, and peace from God our Father, and the Lord Jesus Christ.
Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
8 First, I thank my God, through Jesus Christ, on account of you all, because your faith is spoken of throughout the whole world.
Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya.
9 For God is my witness, whom I serve with my spirit in the gospel of his Son, that, without ceasing, I make mention of you,
Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku.
10 always in my prayers making request, that, if possible, I may at length have a prosperous journey, by the will of God to come to you.
A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.
11 For I greatly desire to see you, that I may impart to you some spiritual gift, in order that you may be established;
Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku.
12 that is, that I may both give and receive comfort, while I am among you, through our common faith.
Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.
13 But, brethren, I do not wish you to be ignorant that I often purposed to come to you, though I have been hindered to the present time, that I might have some fruit among you also, even as among other Gentiles.
Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai.
14 I am a debtor both to the Greeks and to the barbarians; both to the wise and to the unwise.
Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima.
15 So that, as far as I am able, I am ready to preach the gospel to you also, who are in Rome.
Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.
16 For I am not ashamed of the Gospel: for it is the power of God in order to salvation, to every one that believes, to the Jew first, and also to the Greek.
Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,
17 For in it the righteousness of God by faith is revealed, in order to faith: as it is written, He that is justified by faith, shall live.
Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, “Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya.”
18 For the wrath of God is revealed from heaven against all ungodliness and unrighteousness of men, who, by unrighteousness, restrain the truth.
Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su.
19 Because that which may be known of God, is manifest among them; for God has made it manifest to them,
Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.
20 (for, since the creation of the world, his attributes, which are invisible, are clearly seen, being perceived through the things that are made, both his eternal power and divinity, ) that they may be without excuse; (aïdios g126)
Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. (aïdios g126)
21 because, when they knew God, they did not glorify him as God, nor were they thankful; but they became perverse in their reasonings, and their wicked heart was darkened;
Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.
22 professing to be wise, they became foolish,
Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye.
23 and exchanged the glory of the incorruptible God for an image like corruptible man, and birds, and four-footed beasts, and creeping things.
Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.
24 For which reason God delivered them up, in the desires of their hearts, to uncleanness, that they might dishonor their bodies among themselves;
Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu.
25 who exchanged the truth of God for a lie, and worshiped and served the creature more than the Creator, who is blessed forever. Amen. (aiōn g165)
Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
26 For this reason, God delivered them over to vile passions: for their females exchanged their natural use for that which is against nature:
Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace.
27 and in like manner also the males, leaving the natural use of the females, burned in their lusts one toward another, males with males practicing infamous lewdness, and receiving in themselves the due reward of their error.
Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.
28 And as they refused to acknowledge God, God delivered them up to an undiscerning mind, to do detestable things;
Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.
29 as they were filled with all unrighteousness, lewdness, wickedness, covetousness, malice; full of envy, murder, contention, deceit, malignity;
Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi.
30 whisperers, evil-speakers, haters of God, insolent, proud, boasters, inventors of evil things, disobedient to parents;
Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu.
31 without understanding, covenant-breakers, without natural affection, implacable, unmerciful;
Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.
32 who, acknowledging the judgment of God, that those who practice such things are worthy of death, not only do them, but approve those who practice them.
Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.

< Romans 1 >