< Psalms 51 >
1 Have mercy upon me, O God, according to thy loving kindness. According to the multitude of thy tender mercies blot out my transgressions.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
2 Wash me thoroughly from my iniquity, and cleanse me from my sin.
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
3 For I know my transgressions, and my sin is ever before me.
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
4 Against thee, thee only, I have sinned, and done that which is evil in thy sight, that thou may be justified when thou speak, and may prevail when thou are criticized.
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
5 Behold, I was brought forth in iniquity, and in sin my mother conceived me.
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
6 Behold, thou desire truth in the inward parts, and in the hidden part thou will make me to know wisdom.
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
7 Purify me with hyssop, and I shall be clean. Wash me, and I shall be whiter than snow.
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
8 Make me to hear joy and gladness, that the bones which thou have broken may rejoice.
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
9 Hide thy face from my sins, and blot out all my iniquities.
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
10 Create in me a clean heart, O God, and renew a right spirit within me.
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
11 Cast me not away from thy presence, and take not thy holy Spirit from me.
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12 Restore to me the joy of thy salvation, and uphold me with a willing spirit.
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
13 Then I will teach transgressors thy ways, and sinners shall be converted to thee.
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
14 Deliver me from blood guiltiness, O God, thou God of my salvation. And my tongue shall sing aloud of thy righteousness.
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
15 O Lord, open thou my lips, and my mouth shall show forth thy praise.
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
16 For thou delight not in sacrifice, else I would give it. Thou have no pleasure in burnt offering.
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 The sacrifices of God are a broken spirit. A broken and contrite heart, O God, thou will not despise.
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
18 Do good in thy good pleasure to Zion. Build thou the walls of Jerusalem.
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
19 Then thou will delight in the sacrifices of righteousness, in burnt offering and in whole burnt offering. Then they will offer bullocks upon thine altar.
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.