< Job 1 >
1 There was a man in the land of Uz whose name was Job, and that man was perfect and upright, and one who feared God, and turned away from evil.
A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
2 And there were born to him seven sons and three daughters.
Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
3 His substance also was seven thousand sheep, and three thousand camels, and five hundred yoke of oxen, and five hundred she-donkeys, and a very great household, so that this man was the greatest of all the sons of the east.
yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
4 And his sons went and held a feast in the house of each one upon his day, and they sent and called for their three sisters to eat and to drink with them.
’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
5 And it was so, when the days of their feasting were completed, that Job sent and sanctified them, and rose up early in the morning, and offered burnt offerings according to the number of them all. For Job said, It may be that my sons have sinned, and renounced God in their hearts. Thus Job did continually.
Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
6 Now it came to pass on the day when the sons of God came to present themselves before Jehovah, that Satan also came among them.
Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
7 And Jehovah said to Satan, From where do thou come? Then Satan answered Jehovah, and said, From going to and fro on the earth, and from walking up and down on it.
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
8 And Jehovah said to Satan, Have thou considered my servant Job? For there is none like him on the earth, a perfect and an upright man, one who fears God, and turns away from evil.
Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
9 Then Satan answered Jehovah, and said, Does Job fear God for nothing?
Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
10 Have thou not made a hedge about him, and about his house, and about all that he has, on every side? Thou have blessed the work of his hands, and his substance is increased in the land.
Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
11 But put forth thy hand now, and touch all that he has, and he will renounce thee to thy face.
Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
12 And Jehovah said to Satan, Behold, all that he has is in thy power, only upon himself do not put forth thy hand. So Satan went forth from the presence of Jehovah.
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
13 And it fell on a day when his sons and his daughters were eating and drinking wine in their eldest brother's house,
Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
14 that there came a messenger to Job, and said, The oxen were plowing, and the donkeys feeding beside them,
sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
15 and the Sabeans fell upon them, and took them away. Yea, they have slain the servants with the edge of the sword, and only I alone have escaped to tell thee.
sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
16 While he was yet speaking, there came also another, and said, The fire of God fell from heaven, and has burned up the sheep and the servants, and consumed them, and only I alone have escaped to tell thee.
Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
17 While he was yet speaking, there came also another, and said, The Chaldeans made three bands, and fell upon the camels, and have taken them away, yea, and slain the servants with the edge of the sword, and only I alone have escaped to tell thee.
Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
18 While he was yet speaking, there came also another, and said, Thy sons and thy daughters were eating and drinking wine in their eldest brother's house.
Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
19 And, behold, there came a great wind from the wilderness, and smote the four corners of the house, and it fell upon the young men, and they are dead, and only I alone have escaped to tell thee.
sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
20 Then Job arose, and tore his robe, and shaved his head, and fell down upon the ground, and worshiped.
Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
21 And he said, Naked I came out of my mother's womb, and naked I shall return there. Jehovah gave, and Jehovah has taken away, blessed be the name of Jehovah.
ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
22 In all this Job did not sin, nor foolishly accuse God.
Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.