< Psalms 29 >

1 Ascribe to Jehovah, O ye sons of the mighty, ascribe to Jehovah glory and strength.
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Ascribe to Jehovah the glory due to his name. Worship Jehovah in holy array.
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 The voice of Jehovah is upon the waters. The God of glory thunders, even Jehovah upon many waters.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 The voice of Jehovah is powerful. The voice of Jehovah is full of majesty.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 The voice of Jehovah breaks the cedars. Yea, Jehovah breaks in pieces the cedars of Lebanon.
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 He makes them also to skip like a calf, Lebanon and Sirion like a young wild-ox.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 The voice of Jehovah splits the flames of fire.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 The voice of Jehovah shakes the wilderness. Jehovah shakes the wilderness of Kadesh.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 The voice of Jehovah makes the hinds to calve, and strips the forests bare. And in his temple everything says, Glory.
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 Jehovah sat as King at the Flood. Yea, Jehovah sits as King forever.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 Jehovah will give strength to his people. Jehovah will bless his people with peace.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

< Psalms 29 >