< Matthew 24 >
1 And when Jesus departed he was going from the temple. And his disciples came near to exhibit to him the buildings of the temple.
Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
2 But Jesus said to them, Do ye not see all these things? Truly I say to you, there will be left here, no, not a stone upon a stone, that will not be thrown down.
Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
3 And as he sat on the mount of Olives, the disciples came to him privately, saying, Tell us, when will these things be? And what is the sign of thy coming, and of the termination of the age? (aiōn )
Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn )
4 And having answered, Jesus said to them, See that not any man may lead you astray.
Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
5 For many will come in my name, saying, I am the Christ, and will lead many astray.
Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
6 And ye are going to hear of wars and rumors of wars. See that ye not be alarmed, for all the things must happen, but the end is not yet.
Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
7 For nation will rise against nation, and kingdom against kingdom, and there will be famines and plagues and earthquakes in places.
Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
8 But all these things are the beginning of travail.
Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
9 Then they will deliver you up for tribulation, and will kill you, and ye will be hated by all the nations because of my name.
“Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
10 And then many will be caused to stumble, and they will betray each other and will hate each other.
A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
11 And many false prophets will arise, and will lead many astray.
annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
12 And because of the increased lawlessness, the love of the many will become cold.
Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
13 But he who endures to the end, this man will be saved.
amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
14 And this good news of the kingdom will be proclaimed in the whole world for a testimony to all the nations, and then the end will come.
Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
15 When therefore ye see the abomination of desolation that was spoken of through Daniel the prophet, standing in the holy place (let him who reads understand),
“Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
16 then let those in Judea flee to the mountains.
to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
17 Let the man on the housetop not go down to take things from his house.
Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
18 And let the man in the field not return back to take his clothes.
Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
19 And woe to those who have in the womb and to those who suckle in those days.
Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
20 And pray ye that your flight may not happen in winter, nor on a sabbath,
Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
21 for then there will be great tribulation, such as not has happened from the beginning of the world until now, nor, no, it will not happen.
Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
22 And if those days were not shortened, no flesh would be saved. But because of the chosen those days will be shortened.
“Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
23 Then if any man should say to you, Lo, here is the Christ, or, Here, believe ye not.
A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
24 For there will arise false Christs and false prophets, and they will give great signs and wonders, so as to lead astray, if possible, even the chosen.
Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
25 Behold, I have foretold it to you.
Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
26 If therefore they should say to you, Behold, he is in the wilderness, do not go forth. Behold, he is in the inner chambers, do not believe.
“Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
27 For as the lightning comes out from the east, and shines as far as the west, so also will be the coming of the Son of man.
Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
28 For wherever the carcass may be, there the vultures will be gathered together.
Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
29 But straightaway after the tribulation of those days the sun will be darkened, and the moon will not give its light. And the stars will fall from the sky, and the powers of the heavens will be shaken.
“Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
30 And then the sign of the Son of man will appear in the sky. And then all the tribes of the earth will beat the breast, and they will see the Son of man coming in the clouds of the sky with power and much glory.
“A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
31 And he will send forth his agents with a great trumpet sound, and they will gather together his chosen from the four winds, from the boundaries of the heavens-as far as their boundaries.
Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
32 Now learn a parable from the fig tree. When its branch now becomes tender, and sprouts leaves, ye know that the summer is near.
“Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
33 So ye also, when ye see all these things, know that it is near, at the doors.
Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
34 Truly I say to you, this generation will, no, not pass away, until all these things happen.
Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
35 The sky and the earth will pass away, but my words may, no, not pass away.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
36 But about that day and hour no man knows, not even the agents of the heavens, except my Father only.
“Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
37 And as the days of Noah, so also will be the coming of the Son of man.
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
38 For as in the days before the flood they were eating and drinking, marrying and giving in marriage until that day Noah entered into the ark.
Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
39 And they knew not until the flood came, and took them all away. So also will be the coming of the Son of man.
ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
40 Then two men will be in the field, one is taken, and one is left.
Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
41 Two women grinding at the mill, one is taken, and one is left.
Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
42 Watch therefore, because ye know not at what hour your Lord comes.
“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
43 But know this, that if the house-ruler had known in what watch the thief was coming, he would have watched, and would not have allowed his house to be broken into.
Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
44 Because of this ye also be ready, because in that hour ye think not the Son of man comes.
Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
45 Who then is the faithful and wise bondman, whom his lord appointed over his service, to give them the provision on time?
“Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
46 Blessed is that bondman, whom his lord when he comes will find so doing.
Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
47 Truly I say to you, that he will appoint him over all things being possessed by him.
Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
48 But if that evil bondman should say in his heart, My lord is late coming,
Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
49 and should begin to beat the fellow bondmen, and to eat and drink with the drunken,
Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
50 the lord of that bondman will come in a day that he does not expect, and in an hour that he is not aware,
Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
51 and he will cut him in two, and place his share with the hypocrites. There will be the weeping and the gnashing of teeth.
Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.