< Mark 1 >

1 The beginning of the good news of Jesus Christ, the Son of God.
Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
2 As it is written in the prophets, Behold, I send my agent before thy face, who will prepare thy way before thee.
An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
3 The voice of a man crying out in the wilderness: Prepare ye the way of the Lord. Make his paths straight.
“muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
4 It came to pass, that John was immersing in the wilderness and preaching an immersion of repentance for remission of sins.
Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
5 And all the land of Judea and the Jerusalemites went out to him, and they were all immersed by him in the river Jordan, confessing their sins.
Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
6 And John was clothed with camel's hair and a leather belt around his waist, and eating locusts and wild honey.
Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
7 And he preached, saying, A man mightier than I comes after me of whom I am not worthy, having stooped down, to loosen the strap of his shoes.
Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
8 I indeed immersed you in water, but he will immerse you in the Holy Spirit.
Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
9 And it came to pass in those days, that Jesus came from Nazareth of Galilee, and was immersed by John in the Jordan.
A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
10 And straightaway coming up out of the water, he saw the heavens divided, and the Spirit descending upon him as a dove.
Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
11 And a voice occurred out of the heavens, Thou are my beloved Son, in whom I am well pleased.
Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
12 And straightaway the Spirit drives him forth into the wilderness.
Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
13 And he was there in the wilderness forty days tempted by Satan. And he was with the wild beasts. And the agents served him.
ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
14 Now after John was delivered up, Jesus came into Galilee proclaiming the good news of God,
Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
15 and saying, The time is fulfilled, and the kingdom of God has come near. Repent ye, and believe in the good news.
Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
16 And walking beside the sea of Galilee he saw Simon and Andrew his brother, the son of Simon, casting a net in the sea, for they were fishermen.
Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
17 And Jesus said to them, Come ye behind me, and I will make you to become fishermen of men.
Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
18 And straightaway they left the nets, and followed him.
Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
19 And having advanced a little from there he saw James the son of Zebedee, and John his brother, who were also in the boat mending the nets.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
20 And straightaway he called them. And having left their father Zebedee in the boat with the workmen, they went behind him.
Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
21 And they entered into Capernaum, and straightaway on the sabbath day, having entered into the synagogue, he taught.
Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
22 And they were astonished at his teaching, for he was teaching them as having authority, and not as the scholars.
Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
23 And a man was in their synagogue with an unclean spirit. And he cried out,
Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
24 saying, Oh no! What is with us and with thee, Jesus of Nazareth? Did thou come to destroy us? I know thee who thou are, the Holy man of God.
“Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
25 And Jesus rebuked him, saying, Be thou muzzled, and come out of him.
Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
26 And the unclean spirit, having convulsed him and having cried in a great voice, came out of him.
Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
27 And they were all amazed, so as to question among themselves, saying, What is this? What is this new doctrine, that he commands with authority, and the unclean spirits also obey him?
Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
28 And his fame went forth straightaway into the entire region around Galilee.
Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
29 And straightaway, when they came forth out of the synagogue they came into the house of Simon and Andrew, with James and John.
Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
30 But Simon's mother-in-law lay feverish, and straightaway they tell him about her.
Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 And upon coming, having taken hold of her hand, he raised her up and the fever left her. And straightaway she served them.
Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
32 And having become evening when the sun set they brought to him all who were faring badly, and those who were demon-possessed.
A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
33 And the whole city was gathered together near the door.
Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
34 And he healed many who were faring badly with various diseases, and cast out many demons. And he did not allow the demons to speak, because they had recognized him.
Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
35 And having risen early, very much in the night, he came out and departed into a desolate place, and prayed there.
Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
36 And Simon and those with him searched for him.
Siman da abokansa suka fita nemansa.
37 And having found him, they say to him, All are seeking thee.
Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
38 And he says to them, Let us go into the nearby towns, so that I may preach there also. For I came forth for this.
Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
39 And he was preaching in their synagogues in all Galilee, and casting out the demons.
Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
40 And a leper comes to him beseeching him, and kneeling down to him, and saying to him, If thou will thou can make me clean.
Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
41 And Jesus, having felt compassion, having reached out his hand, he touched him, and says to him, I will, be thou clean.
Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
42 And after he spoke, straightaway the leprosy departed from him, and he was cleansed.
Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
43 And having strictly warned him, straightaway he sent him out.
Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
44 And he says to him, See thou say nothing to any man, but go, show thyself to the priest, and bring for thy cleansing the things that Moses commanded for a testimony to them.
“Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
45 But having gone out, he began to proclaim it much, and to spread abroad the matter, so as for him to no longer be able to enter openly into a city, but was outside in desolate places. And they came to him from all directions.
A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.

< Mark 1 >