< Luke 16 >

1 And he also said to his disciples, There was a certain rich man who had a manager, and this man was accused to him as squandering things possessed by him.
Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
2 And having called him, he said to him, What is this I hear about thee? Render the account of thy management, for thou can no longer manage.
Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
3 And the manager said within himself, What shall I do because my lord takes away the management from me? I am not able to dig. I am ashamed to beg.
“Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
4 I know what I will do, so that when I am removed from the management they may receive me into their houses.
Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
5 And having summoned each one of his lord's debtors, he said to the first, How much do thou owe to my lord?
“Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
6 And he said, A hundred measures of olive oil. And he said to him, Receive thy document, and having sat down, quickly write fifty.
“Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
7 Next he said to another, And how much do thou owe? And he said, A hundred measures of wheat. And he says to him, Receive thy document, and write eighty.
“Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
8 And his lord commended the unrighteous manager because he did shrewdly. Because the sons of this age are shrewder in their own generation than the sons of the light. (aiōn g165)
“Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
9 And I say to you, make friends for yourselves from the mammon of unrighteousness, so that, when ye cease, they may receive you into the eternal dwellings. (aiōnios g166)
Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
10 The man faithful in the least is faithful also in much, and the man unrighteous in the least is unrighteous also in much.
“Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
11 If therefore ye did not become faithful in the unrighteous mammon, who will entrust to you what is true?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
12 And if ye did not become faithful in the alien, who will give thine to you?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
13 No servant can serve two masters, for either he will hate the one and love the other, or he will hold to one and despise the other. Ye cannot serve God and mammon.
“Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
14 And the Pharisees, being lovers of money, heard all these things, and they sneered him.
Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
15 And he said to them, Ye are those who declare yourselves righteous in the sight of men, but God knows your hearts. Because what is lofty among men is an abomination in the sight of God.
Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
16 The law and the prophets were until John. From that time the kingdom of God is proclaimed good news, and every man in it is treated aggressively.
“An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
17 But it is easier for the heaven and the earth to pass away, than for one tittle of the law to fall.
Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
18 Every man who divorces his wife and marries another, commits adultery, and every man who marries her who has been divorced from a husband commits adultery.
“Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
19 Now there was a certain rich man, and he was clothed in purple and fine linen, faring sumptuously daily.
“An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
20 But there was a certain poor man named Lazarus, who had been placed near his gate, covered with sores,
A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
21 and longing to be fed with the crumbs that fell from the rich man's table. But even the dogs that came licked his sores.
Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
22 And it came to pass for the poor man to die and be carried by the agents to Abraham's bosom. And the rich man also died and was buried.
“Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
23 And having lifted up his eyes in Hades, being in torments, he sees Abraham from afar and Lazarus by his bosom. (Hadēs g86)
A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
24 And having cried out, he said, Father Abraham, be merciful to me, and send Lazarus, so that he may dip the tip of his finger in water, and cool my tongue, because I am in agony in this flame.
Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
25 But Abraham said, Child, remember that thou in thy lifetime received thy good things, and likewise Lazarus evil things. But now here he is comforted and thou are in agony.
“Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 And besides all these things, between us and you a great chasm is fixed, so that those here who want to cross over to you are not able, nor may those go across from there to us.
Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
27 And he said, I beg thee therefore, father, that thou would send him to my father's house,
“Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
28 for I have five brothers, that he may testify to them, lest they also come into this place of torment.
gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
29 But Abraham says to him, They have Moses and the prophets. Let them hear them.
“Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
30 And he said, No, father Abraham, but if some man would go to them from the dead they will repent.
“Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
31 And he said to him, If they do not listen to Moses and the prophets, neither will they be persuaded if some man would rise from the dead.
“Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”

< Luke 16 >