< Salme 92 >

1 (En Salme. En Sang for Sabbatsdagen.) Det er godt at takke HERREN, lovsynge dit navn, du højeste,
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 ved Gry forkynde din Nåde, om Natten din Trofasthed
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 til tistrenget Lyre, til Harpe, til Strengeleg på Citer!
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 Thi ved dit Værk har du glædet mig, HERRE, jeg jubler over dine Hænders Gerning.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 Hvor store er dine Gerninger, HERRE, dine Tanker såre dybe!
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 Tåben fatter det ikke, Dåren skønner ej sligt.
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 Spirer de gudløse end som Græsset, blomstrer end alle Udådsmænd, er det kun for at lægges øde for stedse,
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 men du er ophøjet for evigt, HERRE.
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 Thi se, dine Fjender, HERRE, se, dine Fjender går under, alle Udådsmænd spredes!
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 Du har løftet mit Horn som Vildoksens, kvæget mig med den friskeste Olie;
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 det fryder mit Øje at se mine Fjender, mit Øre at høre mine Avindsmænd.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 De retfærdige grønnes som Palmen, vokser som Libanons Ceder;
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 plantet i HERRENs Hus grønnes de i vor Guds Forgårde;
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 selv grånende bærer de Frugt, er friske og fulde af Saft
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 for at vidne, at HERREN er retvis, min Klippe, hos hvem ingen Uret findes.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< Salme 92 >