< Salme 66 >

1 (Til sangmesteren. En salme. En sang.) Bryd ud i Jubel for Gud, al Jorden,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 lovsyng hans Navns Ære, syng ham en herlig Lovsang,
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 sig til Gud: "Hvor forfærdelige er dine Gerninger! For din vældige Styrkes Skyld logrer Fjenderne for dig,
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 al Jorden tilbeder dig, de lovsynger dig, lovsynger dit Navn." (Sela)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Kom hid og se, hvad Gud har gjort i sit Virke en Rædsel for Menneskenes Børn.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Han forvandlede Hav til Land, de vandrede til Fods over Strømmen; lad os fryde os højlig i ham.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Han hersker med Vælde for evigt, på Folkene vogter hans Øjne, ej kan genstridige gøre sig store. (Sela)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 I Folkeslag, lov vor Gud, lad lyde hans Lovsangs Toner,
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 han, som har holdt vor Sjæl i Live og ej lod vor Fod glide ud!
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Thi du ransaged os, o Gud, rensede os, som man renser Sølv;
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 i Fængsel bragte du os, lagde Tynge på vore Lænder,
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 lod Mennesker skride hen over vort Hoved, vi kom gennem Ild og Vand; men du førte os ud og bragte os Lindring!
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 Med Brændofre vil jeg gå ind i dit Hus og indfri dig mine Løfter,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 dem, mine Læber fremførte, min Mund udtalte i Nøden.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Jeg bringer dig Ofre af Fedekvæg sammen med Vædres Offerduft, jeg ofrer Okser tillige med Bukke. (Sela)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Kom og hør og lad mig fortælle jer alle, som frygter Gud, hvad han har gjort for min Sjæl!
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Jeg råbte til ham med min Mund og priste ham med min Tunge.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Havde jeg tænkt på ondt i mit Hjerte, da havde Herren ej hørt;
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 visselig, Gud har hørt, han lytted til min bedende Røst.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Lovet være Gud, som ikke har afvist min Bøn eller taget sin Miskundhed fra mig!
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Salme 66 >