< Salme 78 >

1 (En Maskil af Asaf.) Lyt, mit folk til min lære, bøj eders øre til ord fra min Mund;
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 jeg vil åbne min Mund med Billedtale, fremsætte Gåder fra fordums Tid,
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 hvad vi har hørt og ved, hvad vore Fædre har sagt os;
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 vi dølger det ikke for deres Børn, men melder en kommende Slægt om HERRENs Ære og Vælde og Underne, som han har gjort.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Han satte et Vidnesbyrd i Jakob, i Israel gav han en Lov, idet han bød vore Fædre at lade deres Børn det vide,
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 at en senere Slægt kunde vide det, og Børn, som fødtes siden, stå frem og fortælle deres Børn derom,
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 så de slår deres Lid til Gud og ikke glemmer Guds Gerninger, men overholder hans Bud,
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 ej slægter Fædrene på, en vanartet, stridig Slægt, hvis Hjerte ikke var fast, hvis Ånd var utro mod Gud
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 - Efraims Børn var rustede Bueskytter, men svigted på Stridens Dag -
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Gudspagten holdt de ikke, de nægtede at følge hans Lov;
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 hans Gerninger gik dem ad Glemme, de Undere, han lod dem skue.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Han gjorde Undere for deres Fædre i Ægypten på Zoans Mark;
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 han kløvede Havet og førte dem over, lod Vandet stå som en Vold;
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 han ledede dem ved Skyen om Dagen, Natten igennem ved Ildens Skær;
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 han kløvede Klipper i Ørkenen, lod dem rigeligt drikke som af Strømme,
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 han lod Bække rinde af Klippen og Vand strømme ned som Floder.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Men de blev ved at synde imod ham og vække den Højestes Vrede i Ørkenen;
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 de fristede Gud i Hjertet og krævede Mad til at stille Sulten,
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 de talte mod Gud og sagde: "Kan Gud dække Bord i en Ørken?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Se, Klippen slog han, så Vand flød frem, og Bække vælded ud; mon han også kan give Brød og skaffe kød til sit Folk?"
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Det hørte HERREN, blev vred, der tændtes en Ild mod Jakob, ja Vrede kom op mod Israel,
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 fordi de ikke troede Gud eller stolede på hans Frelse.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Da bød han Skyerne oventil, lod Himlens Døre åbne
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 og Manna regne på dem til Føde, han gav dem Himmelkorn;
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Mennesker spiste Englebrød, han sendte dem Mad at mætte sig med.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Han rejste Østenvinden på Himlen, førte Søndenvinden frem ved sin Kraft;
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 Kød lod han regne på dem som Støv og vingede Fugle som Havets Sand,
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 lod dem falde midt i sin Lejr, rundt omkring sine Boliger;
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Og de spiste sig overmætte, hvad de ønskede, lod han dem få.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Men før deres Attrå var stillet, mens Maden var i deres Mund,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 rejste Guds Vrede sig mod dem; han vog deres kraftige Mænd, fældede Israels Ynglinge.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Og dog blev de ved at synde og troede ej på hans Undere.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Da lod han deres Dage svinde i Tomhed og endte brat deres År.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Når han vog dem, søgte de ham, vendte om og spurgte om Gud,
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 kom i Hu, at Gud var deres Klippe, Gud den Allerhøjeste deres Genløser.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 De hyklede for ham med Munden, løj for ham med deres Tunge;
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 deres Hjerter holdt ikke fast ved ham, hans Pagt var de ikke tro.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Og dog er han barmhjertig, han tilgiver Misgerning, lægger ej øde, hans Vrede lagde sig Gang på Gang, han lod ikke sin Harme fuldt bryde frem;
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 han kom i Hu, de var Kød, et Pust, der svinder og ej vender tilbage.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Hvor tit stod de ham ikke imod i Ørkenen og voldte ham Sorg i det øde Land!
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 De fristede alter Gud, de krænkede Israels Hellige;
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 hans Hånd kom de ikke i Hu, de Dag han friede dem fra Fjenden,
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 da han gjorde sine Tegn i Ægypten, sine Undere på Zoans Mark,
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 forvandlede deres Floder til Blod, så de ej kunde drikke af Strømmene,
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 sendte Myg imod dem, som åd dem, og Frøer, som lagde dem øde,
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 gav Æderen, hvad de avlede, Græshoppen al deres Høst,
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 slog deres Vinstokke ned med Hagl, deres Morbærtræer med Frost,
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 prisgav Kvæget for Hagl og deres Hjorde for Lyn.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Han sendte sin Vredesglød mod dem, Harme, Vrede og Trængsel, en Sendefærd af Ulykkesengle;
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 frit Løb gav han sin Vrede, skånede dem ikke for Døden, gav deres Liv til Pris for Pest;
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 alt førstefødt i Ægypten slog han, Mandskraftens Førstegrøde i Kamiternes Telte,
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 lod sit Folk bryde op som en Hjord, ledede dem som Kvæg i Ørkenen,
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 ledede dem trygt, uden Frygt, mens Havet lukked sig over deres Fjender;
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 han bragte dem til sit hellige Land, de Bjerge, hans højre vandt,
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 drev Folkeslag bort foran dem, udskiftede ved Lod deres Land og lod Israels Stammer bo i deres Telte.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Dog fristed og trodsede de Gud den Allerhøjeste og overholdt ikke hans Vidnesbyrd;
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 de faldt fra, var troløse som deres Fædre, svigtede som en slappet Bue,
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 de krænkede ham med deres Offerhøje, æggede ham med deres Gudebilleder.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Det hørte Gud og blev vred følte højlig Lede ved Israel;
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 han opgav sin Bolig i Silo, det Telt, hvor han boede blandt Mennesker;
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 han gav sin Stolthed i Fangenskab, sin Herlighed i Fjendehånd,
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 prisgav sit Folk for Sværdet, blev vred på sin Arvelod;
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Ild fortærede dets unge Mænd, dets Jomfruer fik ej Bryllupssange,
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 dets Præster faldt for Sværdet, dets Enker holdt ikke Klagefest.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Da vågnede Herren som en, der har sovet, som en Helt, der er døvet af Vin;
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 han slog sine Fjender på Ryggen, gjorde dem evigt til Skamme.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Men han fik Lede ved Josefs Telt, Efraims Stamme udvalgte han ikke;
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 han udvalgte Judas Stamme, Zions Bjerg, som han elsker;
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 han byggede sit Tempel himmelhøjt, grundfæstede det evigt som Jorden.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Han udvalgte David, sin Tjener, og tog ham fra Fårenes Folde,
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 hentede ham fra de diende Dyr til at vogte Jakob, hans Folk, Israel, hans Arvelod;
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 han vogtede dem med oprigtigt Hjerte, ledede dem med kyndig Hånd.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Salme 78 >