< Lukas 6 >

1 Men det skete på den næstførste Sabbat, at han vandrede igennem en Sædemark, og hans Disciple plukkede Aks og gned dem med Hænderne og spiste.
A wata ranar Asabbaci, Yesu yana bi ta gonakin hatsi, sai almajiran suka fara kakkarya kan hatsi suna murjewa a hannuwansu suna ci.
2 Men nogle af Farisæerne sagde: "Hvorfor gøre I, hvad det ikke er tilladt at gøre på Sabbaten?"
Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Me ya sa kuke yin abin da doka ta hana yi a ranar Asabbaci?”
3 Og Jesus svarede og sagde til dem: "Have I da ikke læst, hvad David gjorde, da han blev hungrig, han og de, som vare med ham?
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa ba?
4 hvorledes han gik ind i Guds Hus og tog Skuebrødene og spiste og gav også dem, som vare med ham, skønt det ikke er nogen tilladt at spise dem uden Præsterne alene."
Ya shiga gidan Allah, ya ɗauki keɓaɓɓen burodi, sa’an nan ya ci abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka. Ya kuma ba wa abokan tafiyarsa?”
5 Og han sagde til dem: "Menneskesønnen er Herre også over Sabbaten."
Sai Yesu ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum ne Ubangijin Asabbaci.”
6 Men det skete på en anden Sabbat, at han kom ind i Synagogen og lærte. Og der var der en Mand, hvis højre Hånd var vissen.
A wata ranar Asabbaci kuma, Yesu ya shiga majami’a yana koyarwa. To, a nan kuwa akwai wani mutumin da hannun damansa ya shanye.
7 Men de skriftkloge og Farisæerne toge Vare på ham, om han vilde helbrede på Sabbaten, for at de kunde finde noget at anklage ham for.
Farisiyawa da malaman dokoki suka zuba wa Yesu ido, su ga ko zai warkar a ranar Asabbaci, don su sami dalilin zarginsa.
8 Men han vidste deres Tanker; og han sagde til Manden, som havde den visne Hånd: "Rejs dig og stå frem her i Midten!" Og han rejste sig og stod frem.
Amma Yesu ya san abin da suke tunani. Sai ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.” Sai ya tashi ya tsaya.
9 Men Jesus sagde til dem: "Jeg spørger eder, om det er tilladt at gøre godt på Sabbaten eller at gøre ondt, at frelse Liv eller at ødelægge det?"
Yesu ya ce musu, “Ina tambayarku, me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a hallaka shi?”
10 Og han så omkring på dem alle og sagde til ham: "Ræk din Hånd ud!" Og han gjorde det; da blev hans Hånd sund igen som den anden.
Sai ya kalle su duka, sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙe, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
11 Men de bleve fulde af Raseri og talte med hverandre om, hvad de skulde gøre ved Jesus.
Amma Farisiyawa da malaman Doka suka fusata, suka fara tattauna da junansu a kan abin da za su yi wa Yesu.
12 Men det skete i disse Dage, at han gik ud på et Bjerg for at bede; og han tilbragte Natten i Bøn til Gud.
Wata rana, a cikin kwanakin nan, Yesu ya je wani dutse domin yă yi addu’a, ya kuma kwana yana addu’a ga Allah.
13 Og da det blev Dag, hidkaldte han sine Disciple og udvalgte tolv af dem, hvilke han også kaldte Apostle:
Da gari ya waye, sai ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya zaɓi guda goma sha biyu daga cikinsu, waɗanda ya kira su, Manzanni.
14 Simon, hvem han også kaldte Peter, og Andreas, hans Broder, og Jakob og Johannes og Filip og Bartholomæus
Siman (wanda ya kira Bitrus), ɗan’uwansa Andarawus, Yaƙub, Yohanna, Filibus, Bartolomeyu,
15 og Matthæus og Thomas, Jakob, Alfæus's Søn, og Simon, som kaldes Zelotes,
Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Siman wanda ake kira Zilot,
16 Judas, Jakobs Søn, og Judas Iskariot, som blev Forræder.
Yahuda ɗan Yaƙub, da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
17 Og han gik ned med dem og stod på et jævnt Sted, og der var en Skare af hans Disciple og en stor Mængde af Folket fra hele Judæa og Jerusalem og Kysten ved Tyrus og Sidon,
Sai ya sauko tare da su, ya tsaya a wani fili. A can, akwai taro mai yawa na almajiransa, da kuma mutane masu yawan gaske daga ko’ina a Yahudiya, Urushalima da kuma Taya da Sidon da suke bakin teku,
18 som vare komne for at høre ham og helbredes for deres Sygdomme. Og de plagede bleve helbredte fra urene Ånder;
waɗanda suka zo domin su ji shi, a kuma warkar da cututtukansu. Waɗanda suke fama da mugayen ruhohi kuwa aka warkar da su.
19 og hele Skaren søgte at røre ved ham; thi en Kraft gik ud fra ham og helbredte alle.
Kuma dukan mutane suka yi ƙoƙari su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.
20 Og han opløftede sine Øjne på sine Disciple og sagde: "Salige ere I fattige, thi eders er Guds Rige.
Da ya dubi almajiransa, sai ya ce, “Masu albarka ne ku da kuke matalauta, gama mulkin Allah naku ne.
21 Salige ere I, som nu hungre, thi I skulle mættes. Salige ere I, som nu græde, thi I skulle le.
Masu albarka ne ku da kuke jin yunwa yanzu, gama za ku ƙoshi. Masu albarka ne ku da kuke kuka yanzu, gama za ku yi dariya.
22 Salige er I, når Menneskene hade eder, og når de udstøde eder og håne eder og forkaste eders Navn som ondt for Menneskesønnens Skyld.
Masu albarka ne sa’ad da mutane suka ƙi ku, suka ware ku, suka zage ku, suna ce da ku mugaye, saboda Ɗan Mutum.
23 Glæder eder på den Dag og jubler; thi se, eders Løn er stor i Himmelen. Thi på samme Måde gjorde deres Fædre ved Profeterne.
“Ku yi farin ciki a wannan rana, ku kuma yi tsalle don murna, saboda ladarku yana da yawa a sama. Gama haka kakanninsu suka yi wa annabawa.
24 Men ve eder, I rige, thi I have allerede fået eders Trøst.
“Amma kaitonku da kuke da arziki, gama kun riga kun sami ta’aziyyarku.
25 Ve eder, I, som nu ere mætte, thi I skulle hungre. Ve eder, I, som nu le, thi I skulle sørge og græde.
Kaitonku da kuke ƙosassu yanzu, gama za ku zauna da yunwa. Kaitonku da kuke dariya yanzu, gama za ku yi makoki da kuka.
26 Ve eder, når alle Mennesker tale godt om eder; thi på samme Måde gjorde deres Fædre ved de falske Profeter.
Kaitonku sa’ad da dukan mutane suna magana mai kyau a kanku, gama haka kakanninsu suka yi da annabawan ƙarya.
27 Men jeg siger eder, I, som høre: Elsker eders Fjender, gører dem godt, som hade eder;
“Amma ina faɗa muku, ku da kuke ji na, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku yi wa masu ƙinku alheri.
28 velsigner dem, som forbande eder, og beder for dem, som krænke eder.
Ku albarkaci waɗanda suke la’anta ku, ku kuma yi wa waɗanda suke wulaƙanta ku addu’a.
29 Den, som slår dig på den ene Kind, byd ham også den anden til; og den, som tager Kappen fra dig, formen ham heller ikke Kjortelen!
In wani ya mare ka a wannan kumatu, juya masa ɗayan ma, in wani ya ƙwace maka babban riga, kada ma ka hana masa’yar cikin ma.
30 Giv enhver, som beder dig; og af den, som tager, hvad dit er, kræve du det ikke igen!
Duk wanda ya roƙe ka abu, ka ba shi. In kuma wani ya yi maka ƙwace, kada ka nema yă mayar maka.
31 Og som I ville, at Menneskene skulle gøre imod eder, ligeså skulle også I gøre imod dem!
Ka yi wa waɗansu abin da kai kake so su yi maka.
32 Og dersom I elske dem, som elske eder, hvad Tak have I derfor? Thi også Syndere elske dem, som dem elske.
“In kana ƙaunar masu ƙaunarka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna ƙaunar waɗanda suke ƙaunarsu.
33 Og dersom I gøre vel imod dem, der gøre vel imod eder, hvad Tak have I derfor? Thi også Syndere gøre det samme.
In kuma kana yin alheri ga masu yi maka ne kaɗai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna yin haka.
34 Og dersom I låne dem, af hvem I håbe at få igen, hvad Tak have I derfor? Thi også Syndere låne Syndere for at få lige igen.
In kana ba da bashi ga mutanen da za su iya biyan ka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma, suna ba da bashi ga masu zunubi, da fata za a biya su tsab.
35 Men elsker eders Fjender, og gører vel, og låner uden at vente noget derfor, så skal eders Løn være stor, og I skulle være den Højestes Børn; thi han er god imod de utaknemmelige og onde.
Amma, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku kuma yi musu alheri, ku ba su bashi, ba da sa zuciya sai an biya ku ba. Ta yin haka ne kawai, za ku sami lada mai yawa, ku kuma zama’ya’yan Mafi Ɗaukaka, gama shi mai alheri ne ga marasa godiya da mugaye.
36 Vorder barmhjertige, ligesom eders Fader er barmhjertig.
Ku zama masu jinƙai, kamar yadda Ubanku mai jinƙai ne.
37 Og dømmer ikke, så skulle I ikke dømmes; fordømmer ikke, så skulle I ikke fordømmes; forlader, så skal der forlades eder;
“Kada ku ɗora wa wani, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yanke wa wani hukunci, ku ma ba za a yanke muku ba. Ku gafarta, ku ma za a gafarta muku.
38 giver, så skal der gives eder. Et godt, knuget, rystet, topfuldt Mål skulle de give i eders Skød; thi med hvad Mål I måle, skal der tilmåles eder igen."
Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har yă yi tozo, yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna da shi, da shi za a auna muku.”
39 Men han sagde dem også en Lignelse: "Mon en blind kan lede en blind? Ville de ikke begge falde i Graven?
Ya kuma faɗa musu wannan misali cewa, “Makaho yana iya jagoran makaho ne? Ba sai dukansu biyu su fāɗa a rami ba?
40 En Discipel er ikke over sin Mester; men enhver, som er fuldt færdig, skal være som sin Mester.
Ɗalibi bai fi malaminsa ba, sai dai kowane ɗalibi wanda ya sami cikakkiyar koyarwa, zai zama kamar malaminsa.
41 Men hvorfor ser du Skæven, som er i din Broders Øje; men Bjælken, som er i dit eget Øje, bliver du ikke var?
“Don me kake duban ɗan tsinke da yake idon ɗan’uwanka, amma ba ka kula da gungumen da yake a naka ido ba?
42 Eller hvorledes kan du sige til din Broder: Broder! lad mig drage Skæven ud, som er i dit Øje, du, som ikke ser Bjælken i dit eget Øje? Du Hykler! drag først Bjælken ud af dit Øje, og da kan du se klart til at drage Skæven ud, som er i din Broders Øje.
Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Ɗan’uwa, bari in cire maka ɗan tsinke da yake idonka,’ alhali kuwa, kai kanka ka kāsa ganin gungumen da yake a naka ido? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen daga idonka, sa’an nan za ka iya gani sosai, ka kuma cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.”
43 Thi der er intet godt Træ, som bærer rådden Frugt, og intet råddent Træ, som bærer god Frugt
“Ba itace mai kyau da yake ba da munanan’ya’ya. Mummunan itace kuma ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
44 Thi hvert Træ kendes på sin egen Frugt; thi man sanker ikke Figener af Torne, ikke heller plukker man Vindruer af en Tornebusk.
Kowane itace da irin’ya’yansa ne ake saninsa. Mutane ba sa tsinke’ya’yan ɓaure daga ƙaya, ko kuwa’ya’yan inabi daga sarƙaƙƙiya.
45 Et godt Menneske fremfører det gode af sit Hjertes gode Forråd, og et ondt Menneske fremfører det onde af sit onde Forråd; thi af Hjertets Overflødighed taler hans Mund.
Mutumin nagari yakan nuna abubuwa nagari daga cikin nagarta da yake a ɓoye a zuciyarsa, mugun mutum kuwa yakan nuna mugayen abubuwa daga muguntar da take a ɓoye a zuciyarsa. Gama baki yakan faɗa abin da ya cika zuciya ne.”
46 Men hvorfor kalde I mig Herre, Herre! og gøre ikke, hvad jeg siger?
“Don me kuke ce da ni, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ amma ba kwa yin abin da na faɗa?
47 Hver den, som kommer til mig og hører mine Ord og gør efter dem, hvem han er lig, skal jeg vise eder.
Zan nuna muku kwatancin mutumin da yakan zo wurina, yă ji kalmomina, yă kuma aikata.
48 Han er lig et Menneske, der byggede et Hus og gravede i Dybden og lagde Grundvolden på Klippen; men da en Oversvømmelse kom, styrtede Floden imod det Hus, og den kunde ikke ryste det; thi det var bygget godt.
Yana kama da mutumin da ya gina gida, wanda ya haƙa ƙasa da zurfi, sa’an nan ya kafa tushen ginin a kan dutse. Da ambaliyar ruwa ta taso, ƙarfin ruwa kuwa ya buga gidan, wannan bai jijjiga shi ba, domin an yi masa tushen gini na ainihi.
49 Men den, som hører og ikke gør derefter, han er lig et Menneske, der byggede et Hus på Jorden, uden Grundvold; og Floden styrtede imod det, og det faldt straks sammen, og dette Hus's Fald blev stort."
Amma wanda yakan ji kalmomina, ba ya kuma aikata su, yana kama da mutumin da ya gina gida a ƙasa, ba tare da ya kafa tushen gini ba. A sa’ad da ƙarfin ruwa ya buga gidan, sai gidan yă rushe, mummunar rushewa kuwa.”

< Lukas 6 >