< Johannes 1 >
1 I Begyndelsen var Ordet, og Ordet var hos Gud, og Ordet var Gud.
Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
2 Dette var i Begyndelsen hos Gud.
Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
3 Alle Ting ere blevne til ved det, og uden det blev end ikke een Ting til af det, som er.
Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
4 I det var Liv, og Livet var Menneskenes Lys.
A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
5 Og Lyset skinner i Mørket, og Mørket begreb det ikke.
Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
6 Der kom et Menneske, udsendt fra Gud, hans Navn var Johannes.
Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
7 Denne kom til et Vidnesbyrd, for at han skulde vidne om Lyset, for at alle skulde tro ved ham.
Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
8 Han var ikke Lyset, men han skulde vidne om Lyset.
Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
9 Det sande Lys, der oplyser hvert Menneske, var ved at komme til Verden.
Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
10 Han var i Verden, og Verden er bleven til ved ham, og Verden kendte ham ikke.
Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
11 Han kom til sit eget, og hans egne toge ikke imod ham.
Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
12 Men så mange, som toge imod ham, dem gav han Magt til at vorde Guds Børn, dem, som tro på hans Navn;
Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
13 hvilke ikke bleve fødte af Blod, ej heller af Køds Villie, ej heller af Mands Villie, men af Gud.
’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
14 Og Ordet blev Kød og tog Bolig iblandt os, og vi så hans Herlighed, en Herlighed, som en enbåren Søn har den fra sin Fader, fuld af Nåde og Sandhed.
Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
15 Johannes vidner om ham og råber og siger: "Ham var det, om hvem jeg sagde: Den, som kommer efter mig, er kommen foran mig; thi han var før mig."
(Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
16 Thi af hans Fylde have vi alle modtaget, og det Nåde over Nåde.
Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
17 Thi Loven blev given ved Moses; Nåden og Sandheden er kommen ved Jesus Kristus.
Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
18 Ingen har nogen Sinde set Gud; den enbårne Søn, som er i Faderens Skød, han har kundgjort ham.
Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
19 Og dette er Johannes's Vidnesbyrd, da Jøderne sendte Præster og Leviter ud fra Jerusalem, for at de skulde spørge ham: "Hvem er du?"
To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
20 Og han bekendte og nægtede ikke, og han bekendte: "Jeg er ikke Kristus."
Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
21 Og de spurgte ham: "Hvad da? Er du Elias?" Han siger: "Det er jeg ikke." "Er du Profeten?" Og han svarede: "Nej."
Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
22 Da sagde de til ham: "Hvem er du? For at vi kunne give dem Svar, som have udsendt os; hvad siger du om dig selv?"
A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
23 Han sagde: "Jeg er en Røst af en, som råber i Ørkenen: Jævner Herrens Vej, som Profeten Esajas har sagt."
Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
24 Og de vare udsendte fra Farisæerne,
To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
25 og de spurgte ham og sagde til ham: "Hvorfor døber du da, dersom du ikke er Kristus, ej heller Elias, ej heller Profeten?"
suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
26 Johannes svarede dem og sagde: "Jeg døber med Vand; midt iblandt eder står den, I ikke kende,
Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
27 han som kommer efter mig, hvis Skotvinge jeg ikke er værdig at løse."
Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
28 Dette skete i Bethania hinsides Jordan, hvor Johannes døbte.
Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
29 Den næste Dag ser han Jesus komme til sig, og han siger: "Se det Guds Lam, som bærer Verdens Synd!
Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
30 Han er den, om hvem jeg sagde: Efter mig kommer en Mand, som er kommen foran mig; thi han var før mig.
Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
31 Og jeg kendte ham ikke; men for at han skulde åbenbares for Israel, derfor er jeg kommen og døber med Vand."
Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
32 Og Johannes vidnede og sagde: "Jeg har set Ånden dale ned som en Due fra Himmelen, og den blev over ham.
Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
33 Og jeg kendte ham ikke; men den, som sendte mig for at døbe med Vand, han sagde til mig: Den, som du ser Ånden dale ned over og blive over, han er den, som døber med den Helligånd.
Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
34 Og jeg har set det og har vidnet, at denne er Guds Søn."
Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
35 Den næste Dag stod Johannes der atter og to af hans Disciple.
Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
36 Og idet han så på Jesus, som gik der, siger han: "Se det Guds Lam!"
Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
37 Og de to Disciple hørte ham tale, og de fulgte Jesus.
Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
38 Men Jesus vendte sig om, og da han så dem følge sig, siger han til dem: "Hvad søge I efter?" Men de sagde til ham: "Rabbi! (hvilket udlagt betyder Mester) hvor opholder du dig?"
Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
39 Han siger til dem: "Kommer og ser!" De kom da og så, hvor han opholdt sig, og de bleve hos ham den Dag; det var ved den Tiende Time.
Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
40 Den ene af de to, som havde hørt Johannes's Ord og havde fulgt ham, var Andreas, Simon Peters Broder.
Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
41 Denne finder først sin egen Broder Simon og siger til ham: "Vi have fundet Messias" (hvilket er udlagt: Kristus).
Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
42 Og han førte ham til Jesus. Jesus så på ham og sagde: "Du er Simon, Johannes's Søn; du skal hedde Kefas" (det er udlagt: Petrus).
Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
43 Den næste Dag vilde han drage derfra til Galilæa; og han finder Filip. Og Jesus siger til ham: "Følg mig!"
Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
44 Men Filip var fra Bethsajda, fra Andreas's og Peters By.
Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
45 Filip finder Nathanael og siger til ham: "Vi have fundet ham, hvem Moses i Loven og ligeså Profeterne have skrevet om, Jesus, Josefs Søn, fra Nazareth."
Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
46 Og Nathanael sagde til ham: "Kan noget godt være fra Nazareth?" Filip siger til ham: "Kom og se!"
Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
47 Jesus så Nathanael komme til sig, og han siger om ham: "Se, det er sandelig en Israelit, i hvem der ikke er Svig."
Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
48 Nathanael siger til ham: "Hvorfra kender du mig?" Jesus svarede og sagde til ham: "Førend Filip kaldte dig, så jeg dig, medens du var under Figentræet."
Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
49 Nathanael svarede ham: "Rabbi! du er Guds Søn, du er Israels Konge."
Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
50 Jesus svarede og sagde til ham: "Tror du, fordi jeg sagde dig, at jeg så dig under Figentræet? Du skal se større Ting end disse."
Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
51 Og han siger til ham: "Sandelig, sandelig, siger jeg eder, I skulle fra nu af se Himmelen åbnet og Guds Engle stige op og stige ned over Menneskesønnen."
Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”