< Lukas 17 >

1 Men han sagde til sine Disciple: "Det er umuligt, at Forargelser ikke skulde komme; men ve den, ved hvem de komme!
Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
2 Det er bedre for ham, om en Møllesten er lagt om hans Hals, og han er kastet i Havet end at han skulde forarge een af disse små.
Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
3 Vogter på eder selv! Dersom din Broder synder, da irettesæt ham; og dersom han angrer, da tilgiv ham!
Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
4 Og dersom han syv Gange om Dagen synder imod dig og syv Gange vender tilbage til dig og siger: Jeg angrer det, da skal du tilgive ham."
In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
5 Og Apostlene sagde til Herren: "Giv os mere Tro!"
Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
6 Men Herren sagde: "Dersom I havde Tro som et Sennepskorn, da kunde I sige til dette Morbærfigentræ: Ryk dig op med Rode, og plant dig i Havet, og det skulde adlyde eder.
Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
7 Men hvem af eder, som har en Tjener, der pløjer eller vogter, siger til ham, når han kommer hjem fra Marken: Gå straks hen og sæt dig til Bords?
“In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
8 Vil han ikke tværtimod sige til ham: Tilbered, hvad jeg skal have til Nadver, og bind op om dig, og vart mig op, medens jeg spiser og drikker; og derefter må du spise og drikke?
Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
9 Mon han takker Tjeneren, fordi han gjorde det, som var befalet? Jeg mener det ikke.
Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
10 Således skulle også I, når I have gjort alle de Ting, som ere eder befalede, sige: Vi ere unyttige Tjenere; kun hvad vi vare skyldige at gøre, have vi gjort."
Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
11 Og det skete, medens han var på Vej til Jerusalem, at han drog midt imellem Samaria og Galilæa.
Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
12 Og da han gik ind i en Landsby, mødte der ham ti spedalske Mænd, som stode langt borte,
Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
13 og de opløftede Røsten og sagde: "Jesus, Mester, forbarm dig over os!"
suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
14 Og da han så dem, sagde han til dem: "Går hen og fremstiller eder for Præsterne!" Og det skete, medens de gik bort, bleve de rensede.
Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
15 Men en af dem vendte tilbage, da han så, at han var helbredt, og priste Gud med høj Røst.
Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
16 Og han faldt på sit Ansigt for hans Fødder og takkede ham; og denne var en Samaritan.
Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
17 Men Jesus svarede og sagde: "Bleve ikke de ti rensede? hvor ere de ni?
Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
18 Fandtes der ingen, som vendte tilbage for at give Gud Ære, uden denne fremmede?"
Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
19 Og han sagde til ham:"Stå op, gå bort; din Tro har frelst dig!"
Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 Men da han blev spurgt af Farisæerne om, når Guds Rige kommer, svarede han dem og sagde: "Guds Rige kommer ikke således, at man kan vise derpå.
Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
21 Ikke heller vil man sige: Se her, eller: Se der er det; thi se, Guds Rige er inden i eder."
Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
22 Men han sagde til Disciplene: "Der skal komme Dage, da I skulle attrå at se en af Menneskesønnens Dage, og I skulle ikke se den.
Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
23 Og siger man til eder: Se der, eller: Se her er han, så går ikke derhen, og løber ikke derefter!
Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
24 Thi ligesom Lynet, når det lyner fra den ene Side af Himmelen, skinner til den anden Side af Himmelen, således skal Menneskesønnen være på sin Dag.
Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
25 Men først bør han lide meget og forkastes af denne Slægt.
Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
26 Og som det skete i Noas Dage, således skal det også være i Menneskesønnens Dage:
“Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
27 De spiste, drak, toge til Ægte, bleve bortgiftede indtil den Dag, da Noa gik ind i Arken, og Syndfloden kom og ødelagde alle.
Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
28 Ligeledes, som det skete i Loths Dage: De spiste, drak, købte, solgte, plantede, byggede;
“Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
29 men på den Dag, da Loth gik ud af Sodoma, regnede Ild og Svovl ned fra Himmelen og ødelagde dem alle:
Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
30 på samme Måde skal det være på den Dag, da Menneskesønnen åbenbares.
“Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
31 På den dag skal den, som er på Taget og har sine Ejendele i Huset, ikke stige ned for at hente dem; og ligeså skal den, som er på Marken, ikke vende tilbage igen!
A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
32 Kommer Loths Hustru i Hu!
Ku tuna fa da matar Lot!
33 Den, som søger at bjærge sit Liv, skal miste det; og den, som mister det, skal beholde Livet.
Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
34 Jeg siger eder: I den Nat skulle to Mænd være på eet Leje; den ene skal tages med, og den anden skal lades tilbage.
Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
35 To Kvinder skulle male på samme Kværn; den ene skal tages med, og den anden skal lades tilbage.
Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
36 To Mænd skulle være på Marken; den ene skal tages med. og den anden skal lades tilbage."
37 Og de svare og sige til ham: "Hvor, Herre?" Men han sagde til dem: "Hvor Ådselet er, der ville også Ørnene samle sig."
Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”

< Lukas 17 >