< 3 Mosebog 10 >

1 Men Arons Sønner Nadab og Abihu tog hver sin Pande, kom Ild i dem og lagde Røgelse derpå og frembar for HERRENs Åsyn fremmed Ild, som han ikke havde pålagt dem.
’Ya’yan Haruna maza, Nadab da Abihu suka ɗauki farantansu, suka sa wuta a ciki, suka zuba turare a kai; suka kuma miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba.
2 Da for Ild ud fra HERRENs Åsyn og fortærede dem, så de døde for HERRENs Åsyn.
Sai wuta ta fito daga Ubangiji ta cinye su, suka kuma mutu a gaban Ubangiji.
3 Moses sagde da til Aron: "Det er det, HERREN talede om, da han sagde: Jeg viser min Hellighed på dem, der står mig nær, og min Herlighed for alt Folkets Øjne!" Og Aron tav.
Sai Musa ya ce Haruna, “Ga abin da Ubangiji yake nufi sa’ad da ya ce, “‘A cikin waɗanda suka kusace ni za a tabbata ni mai tsarki ne; a fuskar dukan mutane za a kuwa girmama ni.’” Haruna ya yi shiru.
4 Da kaldte Moses Misjael og Elzafan, Arons Farbroder, Uzziels Sønner, til sig og sagde til dem: "Kom og bær eders Frænder bort fra Helligdommen uden for Lejren!"
Sai Musa ya kira Mishayel da Elzafan,’ya’yan Uzziyel kawun Haruna, ya ce musu, “Ku zo nan; ku ɗauki’yan’uwanku waje da sansani, daga gaban wuri mai tsarki.”
5 Og de kom og bar dem uden for Lejren i deres Kjortler, som Moses havde sagt.
Sai suka zo suka ɗauke su, suna nan cikin taguwoyinsu, zuwa waje da sansani yadda Musa ya umarta.
6 Men Moses sagde til Aron og hans Sønner Eleazar og Itamar: "I må hverken lade eders Hår vokse frit eller sønderrive eders Klæder, ellers skal I dø og Vrede komme over hele Menigheden; lad eders Brødre, hele Israels Hus, begræde den Brand, HERREN har antændt;
Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku yage tufafinku, don kada ku mutu. Yin haka zai jawo fushin Ubangiji a kan dukan jama’a. Amma dangoginku, wato, dukan Isra’ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya hallaka da wuta.
7 og vig ikke fra Åbenbaringsteltets indgang, ellers skal I dø, thi HERRENs Salveolie er på eder!" Og de gjorde som Moses sagde.
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada ko kuwa ku mutu, domin man Shafan Ubangiji yana kanku.” Saboda haka suka yi kamar yadda Musa ya faɗa.
8 Og HERREN talede til Aron og sagde:
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana da Haruna ya ce,
9 Vin og stærk Drik må hverken du eller dine Sønner drikke, når I gået ind i Åbenbaringsteltet, for at I ikke skal dø. Det skal være eder en evig gyldig Anordning fra Slægt til Slægt,
“Kai da’ya’yanka maza, ba za ku sha ruwan inabi ko wani abu mai sa jiri ba a duk sa’ad da za ku shiga cikin Tentin Sujada, in ba haka ba za ku mutu. Wannan dawwammamiyar farilla ce wa tsararraki masu zuwa.
10 for at I kan gøre Skel mellem det hellige og det, der ikke er helligt, og mellem det urene og det rene,
Dole ku bambanta tsakanin mai tsarki da marar tsarki, tsakanin marar tsabta da mai tsabta,
11 og for at I kan vejlede Israeliterne i alle de Love, HERREN har kundgjort dem ved Moses.
za ku kuma koyar da Isra’ilawa dukan farillan da Ubangiji ya ba su ta wurin Musa.”
12 Og Moses sagde til Aron og hans tilbageblevne Sønner Eleazar og Itamar: "Tag Afgrødeofferet, der er levnet fra HERRENs Ildoffer, og spis det usyret ved Siden af Alteret, thi det er højhelligt;
Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza da suka ragu, “Ku ɗauki ragowar hadaya ta gari wadda aka yi hadaya ta ƙonawa da ita ga Ubangiji ku ci ba tare da yisti ba, a gefen bagaden, gama tsattsarka ne.
13 I skal spise det på et helligt Sted; det er jo din og dine Sønners retmæssige Del af HERRENs Ildofre; thi således er det mig påbudt.
Ku ci shi a tsattsarkan wuri, gama rabonka ne da na’ya’yanka daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji; gama haka aka umarce ni.
14 Og Svingningsbrystet og Offerydelseskøllen skal I spise på et rent Sted, du, dine Sønner og Døtre, thi de er givet dig tillige med dine Sønner som en retmæssig Del af Israeliternes Takofre;
Amma kai da’ya’yanka maza da mata za su iya ci ƙirjin da aka kaɗa, da kuma cinyar da aka miƙa. Ku ci su a wuri mai tsabta; an ba da su gare ku da kuma’ya’yanku a matsayin rabo daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa.
15 Offerydelseskøllen og Svingningsbrystet skal man frembære sammen med de til Ildofre bestemte Fedtdele, for at Svingningen kan udføres for HERRENs Åsyn, og de skal tilfalde dig og dine Sønner tillige med dig som en evig gyldig Rettighed, således som HERREN har påbudt!"
Cinyar da aka miƙa da kuma ƙirjin da aka kaɗa, dole a kawo su tare da ɓangarori kitsen hadayun da aka yi ta wuri wuta, don a kaɗa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa. Wannan zai zama na kullayaumi gare ka da’ya’yanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
16 Og Moses spurgte efter Syndofferbukken, men se, den var opbrændt. Da blev han fortørnet på Eleazar og Itamar, Arons tilbageblevne Sønner, og sagde:
Sa’ad da Musa ya nemi sani game da akuyar hadaya don zunubi, ya kuwa gane cewa an ƙone shi, sai ya yi fushi da Eleyazar da kuma Itamar,’ya’yan Haruna maza da suka ragu, ya kuma yi tambaya,
17 "Hvorfor har I ikke spist Syndofferet på det hellige Sted? Det er jo dog højhelligt, og han har givet eder det. for at I skal borttage Menighedens Skyld og således skaffe dem Soning for HERRENs Åsyn.
“Me ya sa ba ku ci hadaya don zunubi a cikin wuri mai tsarki ba? Mafi tsaki ne; an ba ku ne don a ɗauke laifin jama’a ta wurin yin kafara saboda su a gaban Ubangiji.
18 Se, Blodet deraf er ikke blevet bragt ind i Helligdommens Indre, derfor havde det været eders Pligt at spise det på det hellige Sted, således som jeg har påbudt!"
Da yake ba a kai jininsa cikin wuri mai tsarki ba, ya kamata ku ci akuyar a wuri mai tsarki, kamar yadda na umarta.”
19 Men Aron svarede Moses: "Se, de har i Dag frembåret deres Syndoffer og Brændoffer for HERRENs Åsyn, og en sådan Tilskikkelse har ramt mig! Om jeg i Dag havde spist Syndofferkød, vilde HERREN da have billiget det?"
Sai Haruna ya amsa wa Musa, “Yau sun miƙa hadayarsu don zunubi da kuma hadayarsu ta ƙonawa a gaban Ubangiji, ga kuma irin waɗannan abubuwa da suka same ni, da a ce na ci hadaya don zunubi yau, da zai yi kyau ke nan a gaban Ubangiji?”
20 Da Mose's hørte dette, billigede han det.
Da Musa ya ji haka, sai ya gamsu.

< 3 Mosebog 10 >