< 2 Mosebog 1 >

1 Dette er Navnene på Israels Sønner, der sammen med Jakob kom til Ægypten med deres Familier:
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
2 Ruben, Simeon, Levi og Juda,
Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
3 Issakar, Zebulon og Benjamin,
Issakar, Zebulun da Benyamin;
4 Dan og Naftali, Gad og Aser.
Dan da Naftali; Gad da Asher.
5 Jakobs Efterkommere udgjorde i alt halvfjerdsindstyve, men Josef var i Ægypten.
Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
6 Imidlertid døde Josef og alle hans Brødre og hele dette Slægtled.
Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
7 Men Israeliterne var frugtbare og formerede sig, og de blev mange og overmåde talrige, så at Landet blev fuldt af dem.
amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
8 Da kom der en ny Konge over Ægypten, som ikke vidste noget om Josef;
Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
9 og han sagde til sit Folk: "Se, Israels Folk bliver talrigere og stærkere end vi.
Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
10 Velan, lad os gå klogt til Værks imod dem, for at de ikke skal blive for mange; ellers kan det hænde, når vi kommer i Krig, at de går over til vore Modstandere og kæmper mod os og til sidst forlader Landet!"
Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
11 Så satte man Fogeder over dem til at plage dem med Trællearbejde, og de måtte bygge Forrådsbyer for Farao: Pitom og Ra'amses.
Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
12 Men jo mere man plagede dem, des flere blev de, og des mere bredte de sig, så Ægypterne fik Rædsel for Israeliterne.
Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
13 Og Ægypterne tvang Israeliterne til Trællearbejde
ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
14 og gjorde dem Livet bittert ved hårdt Arbejde med Ler og Tegl og alle Hånde Markarbejde, ved alt det Arbejde, de tvang dem til at udføre for sig.
Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
15 Ægypterkongen sagde da til Hebræerkvindernes Jordemødre, af hvilke den ene hed Sjifra, den anden Pua:
Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
16 "Når I forløser Hebræerkvinderne, skal I se godt efter ved Fødselen, og er det et Drengebarn, tag så Livet af det, men er det et Pigebarn, lad det så leve!"
“Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
17 Men Jordemødrene frygtede Gud og gjorde ikke, som Ægypterkongen havde befalet dem, men lod Drengebørnene leve.
Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
18 Da lod Ægypterkongen Jordemødrene kalde og sagde til dem: "Hvorfor har I båret eder således ad og ladet Drengebørnene leve?"
Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
19 Men Jordemødrene svarede Farao: "Hebræerkvinderne er ikke som de Ægyptiske Kvinder, de har let ved at føde; inden Jordemoderen kommer til dem, har de allerede født!"
Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
20 Og Gud gjorde vel imod Jordemødrene, og Folket blev stort og såre talrigt;
Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
21 og Gud gav Jordemødrene Afkom, fordi de frygtede ham.
Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
22 Da udstedte Farao den Befaling til hele sit Folk: "Alle Drengebørn, der fødes, skal I kaste i Nilen, men Pigebørnene skal I lade leve!"
Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”

< 2 Mosebog 1 >