< Dommer 1 >

1 Efter Josuas Død adspurgte Israelitterne HERREN og sagde: "Hvem af os skal først drage op til Kamp mod Kana'anæerne?"
Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
2 HERREN svarede: "Det skal Juda; se, jeg giver Landet i hans Hånd!"
Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
3 Juda sagde da til sin Broder Simeon: "Drag op med mig i min Lod og lad os sammen kæmpe med Kana'anæerne, så skal jeg også drage med dig ind i din Lod!" Så gik da Simeon med ham.
Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
4 Juda drog nu op, og HERREN gav Kana'anæerne og Perizziterne i deres Hånd, så de slog dem i Bezek, 10000 Mand.
Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
5 Og da de stødte på Adonibezek i Bezek, angreb de ham og slog Kana'anæerne og Perizziterne.
A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
6 Adonibezek flygtede, men de satte efter ham, og da de havde grebet ham, huggede de Tommelfingrene og Tommeltæerne af ham.
Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
7 Da sagde Adonibezek: "Halvfjerdsindstyve Konger med afhugne Tommelfingre og Tommeltæer havde jeg stadig til at sanke Smuler under mit Bord; hvad jeg har gjort, gengælder Gud mig!" Derpå førte man ham til Jerusalem, og der døde han.
Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
8 Og Judæerne angreb og indtog Jerusalem, huggede Indbyggerne ned og stak Ild på Byen.
Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
9 Senere drog Judæerne ned til Kamp mod Kana'anæerne i Bjergene, i Sydlandet og i Lavlandet.
Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
10 Og Juda drog mod Kana'anæerne i Hebron - Hebron hed fordum Kirjat Arba og slog Sjesjaj, Ahiman og Talmaj.
Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
11 Derfra drog han op mod Indbyggerne i Debir, der fordum hed Kirjaf-Sefer.
Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
12 Da sagde Kaleb: "Den, som slår Kirjat Sefer og indtager det, ham giver jeg min Datter Aksa til Hustru!"
Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
13 Og da Kenizziten Otniel, Kalebs yngre Broder, indtog det, gav han ham sin Datter Aksa til Hustru.
Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
14 Men da hun kom til ham, æggede han hende til at bede sin Fader om Agerland. Hun sprang da ned af Æselet, og Kaleb spurgte hende: "Hvad vil du?"
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
15 Hun svarede: "Giv mig en Velsignelse! Siden du har bortgiftet mig i det tørre Sydland, må du give mig Vandkilder!" Da gav Kaleb hende de øvre og de nedre Vandkilder.
Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
16 Moses's Svigerfaders, Keniten Kobabs, Sønner, drog sammen med Judæerne op fra Palmestaden til Arads Ørken og bosatte sig hos Amalekiterne.
Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
17 Juda drog derpå ud med sin Broder Simeon, og de slog Kana'anæerne, som boede i Zefat, og lagde Band på Byen; derfor blev den kaldt Horma.
Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
18 Og Juda indtog Gaza med dets Område, Askalon med dets Område og Ekron med dets Område.
Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
19 Og HERREN var med Juda, så han tog Bjerglandet i Besiddelse; Lavlandets Indbyggere kunde han nemlig ikke drive bort, fordi de havde Jernvogne.
Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
20 Haleb gav de Hebron, som Moses havde sagt. Og han drev de tre Anaksønner bort derfra.
Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
21 Men Jebusiterne, som boede i Jerusalem, fik Judæerne ikke drevet bort, og Jebusiterne bor den Dag i Dag i Jerusalem sammen med Judæerne.
Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
22 Men også Josefs Hus drog op og gik mod Betel; og HERREN var med dem.
To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
23 Da Josefs Hus udspejdede Betel Byen hed fordum Luz
Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
24 fik Spejderne Øje på en Mand, der gik ud af Byen; og de sagde til ham: "Vis os, hvor vi kan komme ind i Byen, så vil vi skåne dig!"
’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
25 Da viste han dem, hvor de kunde komme ind i Byen. Derpå huggede de dens Indbyggere ned, men Manden og hele hans. Slægt lod de drage bort,
Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
26 og Manden begav sig til Hetiternes Land og byggede en By, som han kaldte Luz; og det hedder den endnu den Dag i Dag.
Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
27 Men Indbyggerne i Bet-Sjean og dets Småbyer og i Ta'anak og dets Småbyer, Indbyggerne i Dor og dets Småbyer, i Jibleam og dets Småbyer og i Megiddo og dets Småbyer fik Manasse ikke drevet bort; det lykkedes Kana'anæerne at blive boende i disse Egne.
Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
28 Da Israelitterne blev de stærkeste, gjorde de Kana'anæerne til Hoveriarbejdere, men drev dem ikke bort.
Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
29 Efraim fik ikke Kana'anæerne, som boede i Gezer, drevet bort; men Kana'anæerne blev boende midt iblandt dem i Gezer.
Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
30 Zebulon fik ikke Indbyggerne i Kitron og Nahalol drevet bort; men Kana'anæerne blev boende midt iblandt dem og blev Hoveriarbejdere.
Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
31 Aser fik ikke Indbyggerne i Akko drevet bort, ej heller Indbyggerne i Zidon, Mahalab, Akzib, Afik og Rehob.
Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
32 Men Aseriterne bosatte sig midt iblandt Kana'anæerne, der boede i Landet, thi de magtede ikke at drive dem bort.
kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
33 Naftali fik ikke Indbyggerne i Bet Sjemesj og Bet-Anat drevet bort, men bosatte sig midt iblandt Kana'anæerne, der boede i Landet: Men Indbyggerne i Bet Sjemesj og Bet Anat blev deres Hoveriarbejdere.
Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
34 Amoriterne trængte Daniterne op i Bjergene og lod dem ikke komme ned i Lavlandet;
Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
35 og det lykkedes Amoriterne at blive boende i Har-Heres, Ajjalon og Sja'albim. Men senere, da Josefs Hus fik Overtaget, blev de Hoveriarbejdere.
Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
36 Edomiternes Landemærke strakte sig fra Akrabbimpasset til Sela og højere op.
Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.

< Dommer 1 >