< Josua 1 >

1 Efter at HERRENs Tjener Moses var død, sagde HERREN til Moses's Medhjælper Josua, Nuns Søn:
Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
2 "Min Tjener Moses er død; bryd nu op tillige med hele dette Folk og gå over Jordan derhenne til det Land, jeg vil give dem, Israeliterne.
“Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
3 Ethvert Sted, eders Fod betræder, giver jeg eder, som jeg lovede Moses.
Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
4 Fra Ørkenen og Libanon til den store Flod, Eufratfloden, hele Hetiternes Land, og til det store Hav i Vest skal eders Landemærker nå.
Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
5 Så længe du lever, skal det ikke være muligt for nogen at holde Stand imod dig; som jeg var med Moses, vil jeg være med dig; jeg vil ikke slippe dig og ikke forlade dig.
Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
6 Vær frimodig og stærk, thi du skal skaffe dette Folk det Land i Eje, som jeg tilsvor deres Fædre at ville give dem.
“Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
7 Vær kun helt frimodig og stærk. så du omhyggeligt handler efter hele den Lov, min Tjener Moses pålagde dig, vig ikke derfra til højre eller venstre, for at du må have Lykken med dig i alt, hvad du tager dig for.
Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
8 Denne Lovbog skal ikke vige fra din Mund, og du skal grunde over den Dag og Nat, for at du omhyggeligt kan handle efter alt, hvad der står skrevet i den; thi da vil det gå dig vel i al din Færd, og Lykken vil følge dig.
Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
9 Har jeg ikke budt dig: Vær frimodig og stærk; vær ikke bange og bliv ikke forfærdet, thi HERREN din Gud er med dig i alt, hvad du tager dig for!"
Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
10 Josua bød derpå Folkets Tilsynsmænd:
Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
11 "Gå omkring i Lejren og byd Folket: Sørg for Rejsetæring, thi om tre Dage skal I gå over Jordan derhenne for at drage ind og tage det Land i Besiddelse, som HERREN eders Gud vil give eder i Eje!"
“Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
12 Men til Rubeniterne, Gaditerne og Manasses halve Stamme sagde Josua:
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
13 "Husk på, hvad HERRENs Tjener Moses bød eder, da han sagde: HERREN eders Gud bringer eder nu til Hvile og giver eder Landet her!
“Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
14 Eders Kvinder og Børn og Kvæg skal blive i det Land, Moses gav eder hinsides Jordan; men I selv, alle våbenføre, skal væbnet drage over i Spidsen for eders Brødre og hjælpe dem,
Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
15 indtil HERREN har bragt eders Brødre til Hvile ligesom eder, når også de har taget det Land i Besiddelse, som HERREN eders Gud vil give dem. Så kan I vende tilbage til eders eget Land og tage det i Besiddelse, det, som HERRENs Tjener Moses gav eder østpå hinsides Jordan!"
har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
16 Da svarede de Josua: "Alt, hvad du har pålagt os, vil vi gøre, og vi vil gå overalt, hvor du sender os;
Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
17 som vi har adlydt Moses i alt, vil vi adlyde dig. Måtte kun HERREN din Gud være med dig, som han var med Moses!
Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
18 Enhver, som sætter sig op imod dine Befalinger og ikke adlyder dine Ord i alt, hvad du pålægger ham, skal dø. Vær kun modig og uforsagt!"
Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”

< Josua 1 >