< Esajas 6 >

1 I Kong Uzzijas Dødsår så jeg Herren sidde på en såre høj Trone, og hans Slæb fyldte Helligdommen.
A shekarar da Sarki Uzziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kujerar sarauta a sama cike da ɗaukaka, zatinsa ya cika haikali.
2 Serafer stod hos ham, hver med seks Vinger; med de to skjulte de Ansigtet, med de to Fødderne, og med de to fløj de;
A bisansa akwai serafofi, kowanne yana da fikafikai shida. Fikafikai biyu sun rufe fuskokinsu, da biyu suka rufe ƙafafunsu, biyu kuma da su suke tashi.
3 og de råbte til hverandre: "Hellig, hellig, hellig er Hærskarers HERRE, al Jorden er fuld af hans Herlighed!"
Suna kiran juna, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki! Ubangiji Maɗaukaki ne; duniya ta cika da ɗaukakarsa.”
4 Og Dørstolpernes Hængsler rystede ved Råbet, medens Templet fyldtes af Røg.
Da jin ƙarar muryoyinsu madogarai da madogaran ƙofa suka girgiza, haikali kuma ya cika da hayaƙi.
5 Da sagde jeg: "Ve mig, det er ude med mig, thi jeg er en Mand med urene Læber, og jeg bor i et Folk med urene Læber, og nu har mine Øjne set Kongen, Hærskarers HERRE!"
Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”
6 Men en af Seraferne fløj hen til mig; og han havde i Hånden et glødende Kul, som han med en Tang havde taget fra Alteret;
Sai ɗaya daga cikin serafofin ya yi firiya zuwa wurina tare da garwashi mai wuta a hannunsa, wanda ya ɗiba da arautaki daga bagade.
7 det lod han røre min Mund og sagde: "Se, det har rørt dine Læber; din Skyld er borte, din Synd er sonet!"
Da shi ne ya taɓa bakina ya ce, “Duba, wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.”
8 Så hørte jeg Herren sige: "Hvem skal jeg sende, hvem vil gå Bud for os?" Og jeg sagde: "Her er jeg, send mig!"
Sa’an nan na ji muryar Ubangiji tana cewa, “Wa zan aika? Wa zai tafi mana?” Sai na ce, “Ga ni! Ka aike ni!”
9 Da sagde han: "Gå hen og sig til det folk: Hør kun, dog skal I intet fatte, se kun, dog skal I intet indse!
Ya ce, “Je ka ka faɗa wa wannan mutane, “‘Kome yawan kasa kunne da za ku yi, ba za ku fahimta ba; Kome yawan dubar da za ku yi, ba za ku san abin da yake faruwa ba.’
10 Gør Hjertet sløvt på dette Folk, gør dets Ører tunge, dets Øjne blinde, så det ikke kan se med Øjnene, ej heller høre med Ørene, ej heller fatte med Hjertet og omvende sig og læges."
Ka sa zuciyar mutanen nan ta dushe; kunnuwansu su kurunce, idanunsu kuma su makance. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta da zuciyarsu, su kuma juyo a kuma warkar da su.”
11 Jeg spurgte: "Hvor længe, Herre?" Og han svarede: "Til Byerne er øde, uden Beboere, og Husene uden et Menneske, og Ager jorden ligger som Ørk!"
Sa’an nan na ce, “Har yaushe, ya Ubangiji?” Ya kuma amsa, “Sai an lalatar da biranen ba kowa a ciki, sai an mai da gidaje kangwaye ƙasa kuma ta zama kango ba amfani,
12 Og HERREN vil fjerne Menneskene, og Tomhed skal brede sig i Landet;
sai lokacin da Ubangiji ya kori kowa aka kuma yashe ƙasar gaba ɗaya.
13 og er der endnu en Tiendedel deri, skal også den udryddes som en Terebinte eller Eg, af hvilken en Stub bliver tilbage, når den fældes. Dens Stub er hellig Sæd.
Ko da yake kashi ɗaya bisa goma zai ragu a ƙasar, za tă sāke zama kango. Amma kamar yadda katambiri da itacen oak sukan bar kututturai sa’ad da aka yanke su, haka iri mai tsarkin nan zai zama kututture a ƙasar mai tsarki.”

< Esajas 6 >