< Jeremias 1 >

1 Ord af Jeremias, Hilkijas søn, en af præsterne i Anatot i Benjamins Land,
Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
2 til hvem HERRENs Ord kom i Amons Søns, Kong Josias af Judas, Dage, i hans Herredømmes trettende År,
Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
3 og fremdeles i Josias's Søns, Kong Jojakim af Judas, Dage indtil Slutningen af Josias's Søns, Kong Zedekias af Judas, elevte Regeringsår, til Jerusalems Indbyggere førtes i Landflygtighed i den femte Måned.
da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
4 HERRENs Ord kom til mig således:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
5 Før jeg danned dig i Moderskød, kendte jeg dig; før du kom ud af Moderliv, helligede jeg dig, til Profet for Folkene satte jeg dig.
“Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
6 Men jeg svarede: "Ak, Herre, HERRE, jeg kan jo ikke tale, thi jeg er ung."
Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
7 Så sagde HERREN til mig: "Sig ikke: Jeg er ung! men gå, hvorhen jeg end sender dig, og tal alt, hvad jeg byder dig;
Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
8 frygt ikke for dem, thi jeg er med dig for at frelse dig, lyder det fra HERREN."
Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
9 Og, HERREN udrakte sin Hånd, rørte ved min Mund og sagde til mig: "Nu lægger jeg mine Ord i din Mund.
Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
10 Se, jeg giver dig i Dag Myndighed over Folk og Riger til at oprykke og nedbryde, til at ødelægge og nedrive, til at opbygge og plante."
Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
11 Siden kom HERRENs Ord til mig således: "Hvad ser du, Jeremias?" Jeg svarede: "Jeg ser en Mandelgren."
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
12 Da sagde HERREN til mig: "Du ser ret, thi jeg er årvågen over mit Ord for at fuldbyrde det."
Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
13 Og HERRENs Ord kom atter til mig således: "Hvad ser du?" Jeg svarede: "Jeg ser en sydende Kedel med Fyrsted mod Nord."
Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
14 Da sagde HERREN til mig: "Nordfra skal Ulykke syde ud over alle Landets Indbyggere;
Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
15 thi se, jeg hidkalder alle Nordens Riger, lyder det fra HERREN, og man skal komme og rejse hver sin Trone ved Indgangen til Jerusalems Porte mod alle dets Mure trindt omkring og mod alle Judas Byer;
Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
16 og jeg vil afsige Dom over dem for al deres Ondskab, at de forlod mig, tændte Offerild for fremmede Guder og tilbad deres Hænders Værk.
Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
17 Så omgjorde dine Lænder og stå frem og tal til dem, alt hvad jeg byder dig! Vær ikke ræd for dem, at jeg ikke skal gøre dig ræd for dem!
“Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
18 Og jeg, se, jeg gør dig i Dag til en fast Stad, til en Jernstøtte og en kobbermur mod hele Landet, Judas Konger og Fyrster, Præsterne og Almuen;
Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
19 de skal kæmpe imod dig, men ikke kunne magte dig; thi jeg er med dig for at frelse dig, lyder det fra HERREN."
Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.

< Jeremias 1 >