< Esajas 19 >

1 Et Udsagn om Ægypten. Se, HERREN farer på letten Sky og kommer til Ægypten; Ægyptens Guder bæver for ham, Ægyptens Hjerte smelter i Brystet.
Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
2 Jeg hidser Ægypten mod Ægypten, så de kæmper Broder mod Broder, Ven mod Ven, By mod By, Rige mod Rige.
“Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
3 Ægyptens Forstand står stille, dets Råd gør jeg til intet, så de søger Guder og Manere, Genfærd og Ånder.
Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
4 Jeg giver Ægypten hen i en hårdhjertet Herres Hånd, en Voldskonge bliver deres Hersker, så lyder det fra Herren, Hærskarers HERRE.
Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
5 Vandet i Floden svinder, Strømmen bliver sid og tør;
Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
6 Strømmene udspreder Stank, Ægyptens Floder svinder og tørres; Rør og Siv visner hen,
Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
7 alt Græsset ved Nilbredden dør, al Sæd ved Nilen hentørres, svinder og er ikke mere.
haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
8 Fiskerne sukker og sørger, alle, som meder i Nilen; de, som, sætter Garn i Vandet, gribes af Modløshed.
Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
9 Til Skamme er de, som væver Linned, Heglersker og de, som væver Byssus;
Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
10 Spinderne er sønderknust, hver Daglejer sørger bittert.
Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
11 Kun Dårer er Zoans Øverster, Faraos viseste Rådmænd så dumt et Råd. Hvor kan I sige til Farao: "Jeg er en Ætling af Vismænd, Ætling af Fortidens Konger?"
Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
12 Ja, hvor er nu dine Vismænd? Lad dem dog kundgøre dig og lade dig vide, hvad Hærskarers HERRE har for mod Ægypten!
Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
13 Hans Fyrster blev Dårer: Fyrster i Nof blev Tåber. Ægypten er bragt til at rave af Stammernes Hjørnesten.
Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
14 I dets Indre har HERREN udgydt Svimmelheds Ånd; Ægypten fik de til at rave i al dets Id, som den drukne raver i sit Spy.
Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
15 For Ægypten lykkes intet, hverken for Hoved eller Hale, Palme eller Siv.
Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
16 På hin Dag skal Ægypten blive som Kvinder; det skal ængstes og grue for Hærskarers HERREs svungne Hånd, som han svinger imod det.
A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
17 Judas Land bliver Ægypten en Rædsel; hver Gang nogen minder dem derom, gribes de af Angst for, hvad Hærskarers HERRE har for imod det.
Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
18 På hin Dag skal fem Byer i Ægypten tale Kana'ans Tungemål og sværge ved Hærskarers HERRE; en af dem skal kaldes Ir-Haheres.
A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
19 På hin Dag skal HERREN have et Alter midt i Ægypten og en Stenstøtte ved dets Grænse.
A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
20 Det skal være Tegn og Vidne for Hærskarers HERRE i Ægypten; når de råber til HERREN over dem, som mishandler dem, vil han sende dem en Frelser; han skal stride og udfri dem.
Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
21 Da skal HERREN give sig til Kende for Ægypten, Ægypterne skal lære HERREN at kende på hin Dag; de skal bringe Slagtoffer og Afgrødeoffer og gøre Løfter til HERREN og indfri dem.
Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
22 HERREN skal slå Ægypten, slå og læge; og når de omvender sig til HERREN, bønhører han dem og læger dem.
Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
23 På hin Dag skal der gå en banet Vej fra Ægypten til Assyrien, og Assyrien skal komme til Ægypten og Ægypten til Assyrien, og Ægypten skal tjene Herren sammen med Assyrien.
A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
24 På hin Dag skal Israel selvtredje, sammen med Ægypten og Assyrien, være en Velsignelse midt på Jorden,
A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
25 som Hærskarers HERRE velsigner med de Ord: "Velsignet være Ægypten, mit Folk, og Assyrien, mine Hænders Værk, og Israel, min Arvelod!"
Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”

< Esajas 19 >