< 1 Mosebog 28 >

1 Da kaldte Isak Jakob til sig og velsignede ham, idet han bød ham: "Du må ikke tage dig en Hustru blandt Kana'ans Døtre.
Saboda haka Ishaku ya kira Yaƙub, ya kuma albarkace shi, sa’an nan ya umarce shi ya ce, “Kada ka auri mace daga Kan’ana.
2 Drag til Paddan-Aram, til din Morfader Betuels Hus, og tag dig der en af din Morbroder Labans Døtre til Hustru!
Tashi nan da nan ka tafi Faddan Aram, zuwa gidan mahaifin mahaifiyarka Betuwel. Ka ɗauko wa kanka mata a can daga cikin’ya’ya matan Laban ɗan’uwan mahaifiyarka.
3 Gud den Almægtige velsigne dig og gøre dig frugtbar og give dig et talrigt Afkom, så du bliver til Stammer i Hobetal.
Bari Allah Maɗaukaki yă albarkace ka, yă kuma sa ka yi ta haihuwa ka riɓaɓɓanya har ka zama ƙungiyar jama’o’i.
4 Han give dig og dit Afkom med dig Abrahams Velsignelse, så du får din Udlændigheds Land i Eje, det, Gud skænkede Abraham!"
Bari Allah yă ba ka da kuma zuriyarka albarkar da ya ba wa Ibrahim, don ka amshi ƙasar da kake baƙunci, ƙasar da Allah ya ba wa Ibrahim.”
5 Så lod Isak Jakob fare, og han drog til Paddan-Aram, til Aramæeren Laban, Betuels Søn, som var Broder til Rebekka, Jakobs og Esaus Moder.
Sa’an nan Ishaku ya sallami Yaƙub, ya kuwa tafi Faddan Aram, zuwa wurin Laban ɗan Betuwel mutumin Aram. Laban ne ɗan’uwan Rebeka, wadda take mahaifiyar Yaƙub da Isuwa.
6 Men Esau fik at vide, at Isak havde velsignet Jakob og sendt ham til Paddan-Aram for at tage sig en Hustru der, og at han, da han velsignede ham, havde pålagt ham ikke at tage sig en Hustru blandt Kana'ans Døtre,
Yanzu Isuwa ya san cewa Ishaku ya albarkaci Yaƙub ya kuma aike shi zuwa Faddan Aram don yă auri mata daga can, ya kuma san cewa sa’ad da ya albarkace shi, ya umarce shi cewa, “Kada ka auro wata mace daga cikin Kan’aniyawa,”
7 og at Jakob havde adlydt sin Fader og Moder og var draget til Paddan-Aram.
ya kuma san cewa Yaƙub ya yi biyayya da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa, ya kuwa tafi Faddan Aram.
8 Da skønnede Esau, at Kana'ans Døtre vakte hans Fader Isaks Mishag,
Sai Isuwa ya gane cewa matan Kan’aniyawa ba su gamshi mahaifinsa Ishaku ba;
9 og han gik til Ismael og tog Mahalat, en Datter af Abrahams Søn Ismael og Søster til Nebajot, til Hustru ved Siden af sine andre Hustruer.
saboda haka sai ya tafi wurin Ishmayel ya auri Mahalat,’yar’uwar Nebayiwot da kuma’yar Ishmayel ɗan Ibrahim, ban da matan da yake da su.
10 Så drog Jakob bort fra Be'ersjeba og vandrede ad Karan til.
Yaƙub ya bar Beyersheba ya kama hanyar Haran.
11 På sin Vandring kom han til det hellige Sted og overnattede der, da Solen var gået ned; og han tog en af Stenene på Stedet og brugte den som Hovedgærde og lagde sig til, Hvile der.
Sa’ad da ya kai wani wuri, sai ya dakata domin yă kwana, gama rana ta riga ta fāɗi. Ya ɗauki dutse daga cikin duwatsun wurin, ya sa shi ya zama matashin kansa, sa’an nan ya kwanta don yă yi barci.
12 Da drømte han, og se, på Jorden stod en Stige, hvis Top nåede til Himmelen, og se, Guds Engle steg op og ned ad den;
Ya yi mafarki inda ya ga wata matakalar hawa, tsaye a ƙasa, kanta ta kai sama, mala’ikun Allah kuwa suna hawa, suna sauka a kanta.
13 og HERREN stod foran ham og sagde: "Jeg er HERREN, din Fader Abrahams og Isaks Gud! Det Land, du hviler på, giver jeg dig og dit Afkom;
A can bisantaUbangiji ya tsaya, ya kuma ce, “Ni ne Ubangiji Allah na mahaifinka Ibrahim da kuma Allah na Ishaku. Zan ba ka, kai da kuma zuriyarka, ƙasar da kake kwance a kai.
14 dit Afkom skal blive som Jordens Støv, og du skal brede dig mod Vest og Øst, mod Nord og Syd; og i dig og i din Sæd skal alle Jordens Slægter velsignes;
Zuriyarka za tă zama kamar ƙurar ƙasa, za ka kuma bazu zuwa yamma da kuma gabas, zuwa arewa da kuma kudu. Dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka da kuma ta wurin’ya’yanka.
15 se, jeg vil være med dig og vogte dig, hvorhen du end går og føre dig tilbage til dette Land; thi jeg vil ikke forlade dig, men opfylde alt, hvad jeg har lovet dig!"
Ina tare da kai, zan lura da kai duk inda ka tafi, zan kuma dawo da kai zuwa wannan ƙasa. Ba zan rabu da kai ba sai na cika abin da na yi maka alkawari.”
16 Da Jakob vågnede af sin Søvn, sagde han: "Sandelig, HERREN er på dette Sted, og jeg vidste det ikke!"
Sa’ad da Yaƙub ya farka daga barci, sai ya yi tunani ya ce, “Tabbatacce Ubangiji yana a wannan wuri, ban kuwa sani ba.”
17 Og han blev angst og sagde: "Hvor forfærdeligt er dog dette Sted! Visselig, her er Guds Hus, her er Himmelens Port!"
Ya ji tsoro, ya kuma ce, “Wane irin wuri ne mai banrazana haka! Lalle wannan gidan Allah ne, kuma nan ne ƙofar sama.”
18 Tidligt næste Morgen tog Jakob den Sten, han havde brugt som Hovedgærde rejste den som en Stenstøtte og gød Olie over den.
Kashegari da sassafe, sai Yaƙub ya ɗauki dutsen da ya yi matashin kai da shi, ya kafa shi al’amudi, ya kuma zuba mai a kansa.
19 Og han kaldte dette Sted Betel; før hed Byen Luz.
Ya kira wannan wuri Betel ko da yake dā ana kiran birnin Luz ne.
20 Derpå gjorde Jakob følgende Løfte: "Hvis Gud er med mig og vogter mig på den Vej, jeg skal vandre, og giver mig Brød at spise og Klæder at iføre mig,
Sa’an nan Yaƙub ya yi alkawari cewa, “In Allah zai kasance tare da ni yă kuma lura da ni a wannan tafiya, yă kuma ba ni abinci in ci da tufafi in sa,
21 og hvis jeg kommer uskadt tilbage til min Faders Hus, så skal HERREN være min Gud,
har in dawo lafiya zuwa gidan mahaifina, to, Ubangiji zai zama Allahna
22 og denne Sten, som jeg har rejst som en Støtte, skal være Guds Hus, og af alt, hvad du giver mig, vil jeg give dig Tiende!"
kuma wannan dutsen da na kafa al’amudi, zai zama gidan Allah, kuma dukan abin da ka ba ni zan ba ka kashi ɗaya bisa goma.”

< 1 Mosebog 28 >