< 5 Mosebog 23 >

1 Ingen, der er gildet ved Knusning eller Snit, har Adgang til HERRENS Forsamling.
Duk wanda aka daƙe, ko yanke gabansa, ba zai shiga taron jama’ar Ubangiji ba.
2 Ingen, som er født i blandet Ægteskab, har Adgang til HERRENs Forsamling; end ikke i tiende Led har hans Afkom Adgang til HERRENs Forsamling.
Duk wanda aka haifa ta wurin cikin shege, har tsara ta goma, zuriyarsa ba za su shiga taron jama’ar Ubangiji ba, har zuwa tsara ta goma.
3 Ingen Ammonit eller Moabit har Adgang til HERRENs Forsamling; end ikke i tiende Led har deres Afkom nogen Sinde Adgang til HERRENs Forsamling,
Ba mutumin Ammon, ko mutumin Mowab, ko kuwa wani zuriyarsu da zai shiga taron jama’ar Ubangiji, har tsara ta goma.
4 fordi de ikke kom eder i Møde med Brød eller Vand undervejs, da I drog bort fra Ægypten, og fordi han lejede Bileam, Beors Søn, fra Petor i Aram Nabarajim, imod dig til at forbande dig;
Gama ba su zo sun tarye ku da burodi da ruwa a hanyarku, sa’ad da kuka fito daga Masar ba, sai ma suka yi haya Bala’am ɗan Beyor daga Fetor a Aram-Naharayim yă furta la’ana a kanku.
5 men HERREN din Gud vilde ikke høre på Bileam, og HERREN din Gud forvandlede Forbandelsen til Velsignelse, fordi HERREN din Gud elskede dig.
Amma Ubangiji Allahnku bai saurari Bala’am ba, sai ya mai da la’anar ta koma albarka gare ku, domin Ubangiji Allahnku yana ƙaunarku.
6 Du skal aldrig i Evighed bekymre dig om deres Velfærd og Lykke!
Kada ku yi yarjejjeniyar abuta da su, muddin kuna da rai.
7 Derimod må du ikke afsky Edomiterne, thi det er dine Brødre. Heller ikke Ægypterne må du afsky, thi du har levet som fremmed i deres Land.
Kada ku yi ƙyamar mutumin Edom, gama mutumin Edom ɗan’uwanku ne. Kada ku yi ƙyamar mutumin Masar, domin kun yi zama baƙunta a ƙasarsa.
8 Deres Efterkommere må have Adgang til HERRENs Forsamling i tredje Led.
’Ya’yan da aka haifa musu na tsara ta uku za su iya shiga taron jama’ar Ubangiji.
9 Når du går i Krig mod dine Fjender og lægger dig i Lejr, så vogt dig for alt, hvad der er utilbørligt.
Sa’ad da kuka yi sansani don ku yi yaƙi da abokan gābanku, ku kiyaye kanku daga duk wani abu marar tsabta.
10 Findes der nogen hos dig, der på Grund af en natlig Hændelse ikke er ren, skal han gå uden for Lejren, han må ikke komme ind i Lejren;
In ɗaya daga cikin mazanku ya ƙazantu saboda zubar da maniyyi, sai yă fita daga sansani yă zauna waje da sansani.
11 når det lakker mod Aften, skal han tvætte sig med Vand, og når Solen går ned, må han atter komme ind i Lejren.
Amma yayinda yamma ke gabatowa sai yă wanke kansa, da fāɗuwar rana kuwa sai yă koma cikin sansani.
12 Du skal have en afsides Plads uden for Lejren, hvor du kan gå for dig selv;
Ku keɓe wuri waje da sansani inda za ku iya zuwa don yin bayan gari.
13 og du skal have en Pind i dit Bælte, og når du sætter dig derude, skal du med den grave et Hul og bagefter tildække dine Udtømmelser.
Sai ku ɗauki wani abin tona ƙasa, sa’ad da kuka yi bayan gari, sai ku tona rami, ku rufe bayan garinku.
14 Thi HERREN din Gud drager med midt i din Lejr for at hjælpe dig og give dine Fjender i din Magt; derfor skal din Lejr være hellig, for at han ikke skal se noget hos dig, der vækker Væmmelse, og vende sig fra dig.
Gama Ubangiji Allahnku yana zagawa a cikin sansaninku don yă tsare ku, yă kuma bashe abokan gābanku gare ku. Dole sansaninku yă kasance da tsarki, saboda kada yă ga wani abu marar kyau a cikinku, har yă juya daga gare ku.
15 Du må ikke udlevere en Træl til hans Herre, når han er flygtet fra sin Herre og søger Tilflugt hos dig.
In bawa ya tsere zuwa wurinku don mafaka, kada ku miƙa shi ga ubangidansa.
16 Han må tage Ophold i din Midte på det Sted, han selv vælger, inden dine Porte, hvor han helst vil være, og du må ikke gøre ham Men.
Ku bar shi yă zauna a cikinku a duk inda yake so, da kuma a kowane garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.
17 Ingen af Israels Døtre må være Skøge, og ingen af Israels Sønner må være Mandsskøge.
Kada mutumin Isra’ila ko mutuniyar Isra’ila yă zama karuwar haikali.
18 Du må ikke for at opfylde et Løfte bringe Skøgefortjeneste eller Hundeløn til HERREN din Guds Hus; thi begge dele er HERREN din Gud en Vederstyggelighed.
Kada ku kawo kuɗin a cikin gida Ubangiji Allahnku da aka samu ta wurin karuwanci wanda mace ko namiji ya yi don biyan wani alkawari, domin Ubangiji Allahnku yana ƙyamar su duka.
19 Du må ikke tage Rente af din Broder, hverken af Penge, Fødevarer eller andet, som man kan tage Rente af.
Kada ku nemi ɗan’uwanku yă biya bashin da kuka ba shi da ruwa, ko kuɗi, ko abinci, ko kowane irin abin da yana iya ba da ruwa.
20 Af Udlændinge må du tage Rente, men ikke af din Broder, hvis HERREN din Gud skal velsigne dig i alt, hvad du tager dig for i det Land, du skal ind og tage i Besiddelse.
Za ku iya nemi ruwa a bashin da kuka ba baƙo, amma ba ɗan’uwanku mutumin Isra’ila ba, domin Ubangiji Allahnku yă sa muku albarka a kowane abin da kuka sa hannunku a kai, a ƙasar da kuke shiga ku ci gādonta.
21 Når du aflægger et Løfte til HERREN din Gud, må du ikke tøve med at indfri det; thi ellers vil HERREN din Gud kræve det af dig, og du vil pådrage dig Skyld.
In fa kuka yi alkawari ga Ubangiji Allahnku, to, kada ku yi jinkirin cikawa, gama tabbatacce Ubangiji Allahnku zai neme shi daga gare ku, za ku kuma zama masu laifin zunubi.
22 Men hvis du undlader at aflægge Løfter, pådrager du dig ingen Skyld.
Amma in ba ku yi alkawari ba, ba kuwa zai zama muku zunubi ba.
23 Hvad du engang har sagt, skal du holde, og du skal gøre, hvad du frivilligt har lovet HERREN din Gud, hvad du har udtalt med din Mund.
Duk abin da ya fita daga bakinku, sai ku lura ku cika shi, kamar yadda kuka yarda da kanku, kuka yi alkawarin ga Ubangiji Allahnku da bakinku.
24 Når du kommer ind i din Næstes Vingård, må du spise alle de Druer, du har Lyst til, så du bliver mæt; men du må ingen komme i din Kurv.
In kun shiga gonar inabin maƙwabcinku, za ku iya cin inabin da kuke so, amma kada ku sa wani a kwandonku.
25 Når du går igennem din Næstes Sæd, må du plukke Aks med din Hånd, men du må ikke komme til din Næstes Sæd med Segl.
In kun shiga gonar hatsin maƙwabcinku, za ku iya murmure tsabar da hannuwanku, amma kada ku sa lauje ku yanka hatsinsa da yake tsaye.

< 5 Mosebog 23 >