< Lukas 8 >

1 Og det skete i Tiden derefter, at han rejste igennem Byer og Landsbyer og prædikede og forkyndte Evangeliet om Guds Rige, og med ham de tolv
Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
2 og nogle Kvinder, som vare helbredede fra onde Aander og Sygdomme, nemlig: Maria, der kaldes Magdalene, af hvem syv onde Aander vare udfarne;
mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
3 og Johanna, Herodes's Husfoged Kuzas Hustru, og Susanna og mange andre, som tjente dem med, hvad de ejede.
da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
4 Men da en stor Skare kom sammen, og de droge til ham fra de forskellige Byer, sagde han ved en Lignelse:
Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
5 „En Sædemand gik ud at saa sin Sæd; og idet han saaede, faldt noget ved Vejen og blev nedtraadt, og Himmelens Fugle aade det op.
“Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
6 Og noget faldt paa Klippen; og da det voksede op, visnede det, fordi det ikke havde Væde.
Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
7 Og noget faldt midt iblandt Torne, og Tornene voksede op med og kvalte det.
Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
8 Og noget faldt i den gode Jord, og det voksede op og bar hundrede Fold Frugt.‟ Da han sagde dette, raabte han: „Den, som har Øren at høre med, han høre!‟
Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
9 Men hans Disciple spurgte ham, hvad denne Lignelse skulde betyde?
Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
10 Og han sagde: „Eder er det givet at kende Guds Riges Hemmeligheder, men de andre i Lignelser, for at de, skønt seende, ikke skulle se, og, skønt hørende, ikke skulle forstaa.
ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
11 Men dette er Lignelsen: Sæden er Guds Ord.
To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
12 Men de ved Vejen ere de, som høre det; derefter kommer Djævelen og tager Ordet bort af deres Hjerte, for at de ikke skulle tro og blive frelste.
Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
13 Men de paa Klippen ere de, som modtage Ordet med Glæde, naar de høre det, og disse have ikke Rod; de tro til en Tid og falde fra i Fristelsens Tid.
Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
14 Men det, som faldt iblandt Torne, det er dem, som have hørt og saa gaa hen og kvæles under Livets Bekymringer og Rigdom og Nydelser og ikke bære moden Frugt.
Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
15 Men det i den gode Jord, det er dem, som, naar de have hørt Ordet, beholde det i et smukt og godt Hjerte og bære Frugt i Udholdenhed.
Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
16 Men ingen, som tænder et Lys, skjuler det med et Kar eller sætter det under en Bænk; men han sætter det paa en Lysestage, for at de, som komme ind, kunne se Lyset.
Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
17 Thi der er ikke noget skjult, som jo skal blive aabenbart; og ikke noget lønligt, som jo skal blive kendt og komme for Lyset.
Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
18 Ser derfor til, hvorledes I høre; thi den, som har, ham skal der gives; og den, som ikke har, fra ham skal endog det tages, han synes at have.‟
Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
19 Men hans Moder og Brødre kom til ham og kunde ikke naa frem til ham for Skaren.
Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
20 Og det blev ham meddelt: „Din Moder og dine Brødre staa udenfor og begære at se dig.‟
Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
21 Men han svarede og sagde til dem: „Min Moder og mine Brødre ere disse, som høre Guds Ord og gøre efter det.‟
Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
22 Og det skete en af de Dage, at han gik om Bord i et Skib tillige med sine Disciple, og han sagde til dem: „Lader os fare over til hin Side af Søen; ‟ og de sejlede ud.
Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
23 Men medens de sejlede, faldt han i Søvn; og en Stormvind for ned over Søen, og Skibet blev fuldt af Vand, og de vare i Fare.
Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
24 Da traadte de hen og vækkede ham og sagde: „Mester, Mester! vi forgaa.‟ Men han stod op og truede Vinden og Vandets Bølger; og de lagde sig, og det blev blikstille.
Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
25 Og han sagde til dem: „Hvor er eders Tro?‟ Men de frygtede og undrede sig og sagde til hverandre: „Hvem er dog denne, siden han byder baade over Vindene og Vandet, og de ere ham lydige?‟
Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
26 Og de sejlede ind til Gadarenernes Land, som ligger lige over for Galilæa.
Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
27 Men da han traadte ud paa Landjorden, mødte der ham en Mand fra Byen, som i lang Tid havde været besat af onde Aander og ikke havde haft Klæder paa og ikke opholdt sig i Hus, men i Gravene.
Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
28 Men da han saa Jesus, raabte han og faldt ned for ham og sagde med høj Røst: „Hvad har jeg med dig at gøre, Jesus, den højeste Guds Søn? jeg beder dig om, at du ikke vil pine mig.‟
Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
29 Thi han bød den urene Aand at fare ud af Manden; thi i lange Tider havde den revet ham med sig, og han blev bunden med Lænker og Bøjer og bevogtet, og han sønderrev, hvad man bandt ham med, og dreves af den onde Aand ud i Ørkenerne.
Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
30 Men Jesus spurgte ham og sagde: „Hvad er dit Navn?‟ Men han sagde: „Legion‟; thi mange onde Aander vare farne i ham.
Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
31 Og de bade ham om, at han ikke vilde byde dem at fare ned i Afgrunden; (Abyssos g12)
Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos g12)
32 men der var sammesteds en stor Hjord Svin, som græssede paa Bjerget; og de bade ham om, at han vilde tilstede dem at fare i dem; og han tilstedte dem det.
Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
33 Men de onde Aander fore ud af Manden og fore i Svinene, og Hjorden styrtede sig ned over Brinken ud i Søen og druknede.
Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
34 Men da Hyrderne saa det, som var sket, flyede de og forkyndte det i Byen og paa Landet.
Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
35 Da gik de ud for at se det, som var sket, og de kom til Jesus og fandt Manden, af hvem de onde Aander vare udfarne, siddende ved Jesu Fødder, paaklædt og ved Samling; og de frygtede.
Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Og de, som havde set det, fortalte dem, hvorledes den besatte var bleven frelst.
Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
37 Og hele Mængden fra Gadarenernes Omegn bad ham om, at han vilde gaa bort fra dem; thi de vare betagne af stor Frygt. Men han gik om Bord i et Skib og vendte tilbage igen.
Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
38 Men Manden, af hvem de onde Aander vare udfarne, bad ham om, at han maatte være hos ham; men han lod ham fare og sagde:
Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
39 „Vend tilbage til dit Hus, og fortæl, hvor store Ting Gud har gjort imod dig.‟ Og han gik bort og kundgjorde over hele Byen, hvor store Ting Jesus havde gjort imod ham.
“Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
40 Men det skete, da Jesus kom tilbage, tog Skaren imod ham; thi de ventede alle paa ham.
Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
41 Og se, der kom en Mand, som hed Jairus, og han var Forstander for Synagogen; og han faldt ned for Jesu Fødder og bad ham komme ind i hans Hus;
Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
42 thi han havde en enbaaren Datter, omtrent tolv Aar gammel, og hun droges med Døden. Men idet han gik, trængte Skarerne sig sammen om ham.
saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
43 Og en Kvinde, som havde haft Blodflod i tolv Aar og havde kostet al sin Formue paa Læger og ikke kunde blive helbredet af nogen,
Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
44 hun gik til bagfra og rørte ved Fligen af hans Klædebon, og straks standsedes hendes Blodflod.
Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
45 Og Jesus sagde: „Hvem var det, som rørte ved mig?‟ Men da alle nægtede det, sagde Peter og de, som vare med ham: „Mester! Skarerne trykke og trænge dig, og du siger: Hvem var det, som rørte ved mig?‟
Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
46 Men Jesus sagde: „Der rørte nogen ved mig; thi jeg mærkede, at der udgik en Kraft fra mig.‟
Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
47 Men da Kvinden saa, at det ikke var skjult, kom hun bævende og faldt ned for ham og fortalte i alt Folkets Paahør, af hvad Aarsag hun havde rørt ved ham, og hvorledes hun straks var bleven helbredet.
Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
48 Men han sagde til hende: „Datter! din Tro har frelst dig; gaa bort med Fred!‟
Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
49 Medens han endnu talte, kommer der en fra Synagogeforstanderens Hus og siger til ham: „Din Datter er død; umag ikke Mesteren!‟
Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
50 Men da Jesus hørte det, svarede han ham: „Frygt ikke; tro blot; saa skal hun blive frelst.‟
Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
51 Men da han kom til Huset, tillod han ingen at gaa ind med sig uden Peter og Johannes og Jakob og Pigens Fader og Moder.
Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
52 Og de græd alle og holdt Veklage over hende; men han sagde: „Græder ikke; hun er ikke død, men sover.‟
Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
53 Og de lo ad ham; thi de vidste, at hun var død.
Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
54 Men han greb hendes Haand og raabte og sagde: „Pige, staa op!‟
Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
55 Og hendes Aand vendte tilbage, og hun stod straks op; og han befalede, at de skulde give hende noget at spise.
Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
56 Og hendes Forældre bleve forfærdede; men han bød dem, at de ikke maatte sige nogen det, som var sket.
Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.

< Lukas 8 >