< Lukas 5 >

1 Men det skete, da Folkeskaren trængte sig sammen om ham og hørte Guds Ord, og han stod ved Genezareths Sø,
Ya zama sa'adda mutane sun taru a wurin Yesu suna sauraron maganar Allah, yana kuma yana tsaye a bakin tabkin Janisarata.
2 da saa han to Skibe staa ved Søen; men Fiskerne vare gaaede fra dem og toede Garnene.
Ya ga jiragen ruwa biyu tsaye a bakin tabkin. Masu kamun kifin kuwa sun fita daga cikin jiragen suna wanke tarunsu.
3 Og han gik om Bord i et af Skibene, som var Simons, og bad ham at lægge lidt fra Land; og han satte sig og lærte Skarerne fra Skibet.
Yesu ya shiga daya daga cikn jiragen wanda shike na Bitrus ne, sai ya umarce shi ya dan zakuda da jirgin daga bakin tabkin kadan zuwa cikin ruwa. Sai ya zauna ya kuma koya wa mutane daga cikin jirgin.
4 Men da han holdt op med at tale, sagde han til Simon: „Far ud paa Dybet, og kaster eders Garn ud til en Dræt!‟
Da ya gama magana, ya ce wa Siman, “Zakuda jirgin zuwa wuri mai zurfi sa'annan ka zuba tarunka domin kamu.”
5 Og Simon svarede og sagde til ham: „Mester! vi have arbejdet hele Natten og fik intet; men paa dit Ord vil jeg kaste Garnene ud.‟
Siman ya amsa ya ce, “Ubangiji, mun yi aiki dukan dare bamu kama komai ba, amma bisa ga maganarka, zan jefa tarun.”
6 Og da de gjorde det, fangede de en stor Mængde Fisk, og deres Garn sønderreves.
Da sun yi haka, suka kama kifaye da yawan gaske, har tarunsu suna yagewa.
7 Og de vinkede ad deres Stalbrødre i det andet Skib, at de skulde komme og hjælpe dem; og de kom, og de fyldte begge Skibene, saa at de vare nær ved at synke.
Sai suka roki abokan aikinsu da ke a dayan jirgin su zo su taimake su. Suka zo sun cika jiragen biyu da kifaye, har suka fara nutsewa.
8 Men da Simon Peter saa det, faldt han ned for Jesu Knæ og sagde: „Gaa bort fra mig, thi jeg er en syndig Mand, Herre!‟
Amma Siman Bitrus, da ya ga haka, ya russuna a gaban Yesu, yana cewa, “Ka rabu da ni Ubangiji, gama ni mai zunubi ne.”
9 Thi en Rædsel var paakommen ham og alle dem, som vare med ham, over den Fiskedræt, som de havde faaet;
Domin ya yi mamaki, da dukan wadanda suke tare da shi, sabili da yawan kifaye da suka kama.
10 ligeledes ogsaa Jakob og Johannes, Zebedæus's Sønner, som vare Simons Stalbrødre. Og Jesus sagde til Simon: „Frygt ikke, fra nu af skal du fange Mennesker.‟
Wannan ya hada da Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi abokan aikin Siman. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, domin daga yanzu, za ka kama mutane.”
11 Og de lagde Skibene til Land og forlode alle Ting og fulgte ham.
Da sun kawo jiragensu waje kan kasa, suka bar komai suka kuma bi shi.
12 Og det skete, medens han var i en af Byerne, se, da var der en Mand fuld af Spedalskhed; og da han saa Jesus, faldt han paa sit Ansigt, bad ham og sagde: „Herre! om du vil, kan du rense mig.‟
Sa'adda yana daya daga cikin biranen, wani mutum dauke da kuturta yana nan wurin. Da ya ga Yesu, ya fadi bisa fuskarsa kasa yana rokansa, yana cewa, “Ubangji, idan ka yarda, za ka iya tsarkake ni.”
13 Og han udrakte Haanden og rørte ved ham og sagde: „Jeg vil; bliv ren!‟ Og straks forlod Spedalskheden ham.
Yesu ya mika hanunsa ya taba shi, yana cewa, “Na yarda. Ka tsarkaka.” Sai nan da nan, kuturtar ta rabu da shi.
14 Og han bød ham, at han skulde ikke sige det til nogen, men „gaa bort, og fremstil dig for Præsten, og offer for din Renselse, saaledes som Moses har befalet, til Vidnesbyrd for dem!‟
Ya umarce shi kada ya gaya wa kowa, amma ya ce ma sa, “Tafi ka nuna kanka ga firist sa'annan ka mika hadaya domin tsarkakewarka, kamar yadda Musa ya umarta, a matsayin shaida a garesu.”
15 Men Rygtet om ham udbredte sig end mere, og store Skarer kom sammen for at høre og for at helbredes for deres Sygdomme.
Amma labarinsa ya bazu nesa, taron mutane da yawa kuma suka zo wurinsa domin su ji shi, su kuma samu warkarwa daga cututtukansu.
16 Men han gik bort til Ørkenerne og bad.
Amma ya kan janye zuwa wuraren da babu kowa ya yi addu'a.
17 Og det skete en af de Dage, at han lærte, og der sad Farisæere og Lovlærere, som vare komne fra enhver Landsby i Galilæa og Judæa og fra Jerusalem; og Herrens Kraft var hos ham til at helbrede.
Ya zama daya a cikin kwanakin da yake koyarwa, akwai Farisawa da malaman attaura da ke zaune a wurin wandanda suka zo daga kauyukan da suke kewaye da Galili da Yahudiya da kuma birnin Urushalima. Ikon Ubangiji yana tare da shi domin warkarwa.
18 Og se, nogle Mænd bare paa en Seng en Mand, som var værkbruden, og de søgte at bære ham ind og lægge ham foran ham.
A lokacin nan, wasu mutane suka zo dauke da wani mutum shanyayye a kan tabarma, suka kuma nemi yadda za su shigar da shi ciki, su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Og da de ikke fandt nogen Vej til at bære ham ind for Skarens Skyld, stege de op oven paa Taget og firede ham tillige med Sengen ned imellem Tagstenene midt iblandt dem foran Jesus.
Ba su iya samun hanyar da za su shigar da shi ba saboda taron, sai suka hau saman gidan, suka saukar da shi daga rufin, a kan tabarman sa, zuwa tsakiyar mutanen, dai dai a gaban Yesu.
20 Og da han saa deres Tro, sagde han: „Menneske! dine Synder ere dig forladte.‟
Da ya ga bangaskiyarsu, Yesu ya ce, “Maigida, an gafarta zunubanka.”
21 Og de skriftkloge og Farisæerne begyndte at tænke saaledes ved sig selv: „Hvem er denne, som taler Gudsbespottelser? Hvem kan forlade Synder, uden Gud alene?‟
Marubuta da Farisawa suka fara sukar wannan, suna cewa, “Wanene wannan da ke sabo? Wa zai iya gafarta zunubi, idan ba Allah kadai ba?”
22 Men da Jesus kendte deres Tanker, svarede han og sagde til dem: „Hvad tænke I paa i eders Hjerter?
Amma da Yesu ya fahimci abin da suke tunani, sai ya amsa ya ce masu, “Don me kuke sukar wannan a zuciyarku?
23 Hvilket er lettest at sige: Dine Synder ere dig forladte? eller at sige: Staa op og gaa?
Wanne ne ya fi sauki a ce, 'An yafe zunubanka' ko kuwa a ce, 'Tashi ka yi tafiya?”
24 Men for at I skulle vide, at Menneskesønnen har Magt paa Jorden til at forlade Synder, ‟ saa sagde han til den værkbrudne: „Jeg siger dig, staa op, og tag din Seng, og gaa til dit Hus!‟
Amma domin ku sani cewa Dan Mutum yana da yancin gafarta zunubai a duniya, na ce maka, 'Tashi, dauki tabarmanka, ka tafi gidanka.'”
25 Og han stod straks op for deres Øjne og tog det, som han laa paa, og gik hen til sit Hus og priste Gud.
Nan take, ya tashi a gabansu ya dauki tabarma da yake kwance; sai ya koma gidansa, yana daukaka Allah.
26 Og Forfærdelse betog alle, og de priste Gud; og de bleve fulde af Frygt og sagde: „Vi have i Dag set utrolige Ting.‟
Kowa yana ta mamaki kuma suka daukaka Allah. Suna cike da tsoro, suna cewa, “Yau mun ga abubuwan al'ajibi.”
27 Og derefter gik han ud og saa en Tolder ved Navn Levi sidde ved Toldboden, og han sagde til ham: „Følg mig!‟
Bayan wadannan abubuwa sun faru, Yesu ya fito daga can sai ya ga wani mai karban haraji mai suna Lawi yana zama a wurin karban haraji. Ya ce masa, “Ka biyo ni.”
28 Og han forlod alle Ting og stod op og fulgte ham.
Sai Lawi ya bar komai, ya tashi, ya bi shi.
29 Og Levi gjorde et stort Gæstebud for ham i sit Hus; og der var en stor Skare af Toldere og andre, som sade til Bords med dem.
Lawi kuma ya shirya gagarumar liyafa a gidansa, kuma akwai masu karban haraji da yawa a nan, da wasu mutane da ke zama a gaban teburin liyafar suna cin abinci tare da su.
30 Og Farisæerne og deres skriftkloge knurrede imod hans Disciple og sagde: „Hvorfor spise og drikke I med Toldere og Syndere?‟
Amma Farisawa da Marubuta suka fara korafi ga almajiransa, suna cewa, “Don menene kuna ci da sha tare da masu karban haraji da mutane masu zunubi?”
31 Og Jesus svarede og sagde til dem: „De raske trænge ikke til Læge, men de syge.
Yesu ya amsa masu, “Masu lafiya basu bukatar likita, wadanda ke marasa lafiya kadai ke bukatar likita.
32 Jeg er ikke kommen for at kalde retfærdige, men Syndere til Omvendelse.‟
Ban zo domin kiran masu adalci ba, amma na zo ne domin kiran masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Men de sagde til ham: „Johannes's Disciple faste ofte og holde Bønner og Farisæernes ligesaa; men dine spise og drikke?‟
Sun ce masa, “Almajiran Yahaya sukan yi azumi da addu'a, kuma almajiran Farisawa ma sukan yi haka. Amma almajiranka suna ci suna sha?”
34 Men Jesus sagde til dem: „Kunne I vel faa Brudesvendene til at faste, saa længe Brudgommen er hos dem?
Yesu ya ce masu, “Akwai wanda zai sa abokan ango su yi azumi, a lokacin da shi ango yana tare da su?
35 Men der skal komme Dage, da Brudgommen bliver tagen fra dem; da skulle de faste i de Dage.‟
Amma kwanaki na zuwa wadanda za a dauke ango daga wurinsu, a kwanakin za su yi azumi.”
36 Men han sagde ogsaa en Lignelse til dem: „Ingen river en Lap af et nyt Klædebon og sætter den paa et gammelt Klædebon; ellers river han baade det nye sønder, og Lappen fra det nye vil ikke passe til det gamle.
Sai Yesu ya sake fada masu wani misali. “Babu wanda zai yage kyalle daga sabuwar tufa, ya kuma yi amfani da ita ya dinka tsohuwar tufa. Idan ya yi hakannan, zai yage sabuwar tufar, kuma kyallen daga sabuwar tufar ba zai dace da kyallen tsohuwar tufar ba.
37 Og ingen kommer ung Vin paa gamle Læderflasker; ellers sprænger den unge Vin Læderflaskerne, og den spildes, og Læderflaskerne ødelægges.
Kuma, babu mutum da zai sa sabon ruwan inabi a cikin tsofafin salkuna. Idan ya yi haka, sabon ruwan inabin zai fasa salkunan, kuma ruwan inabin din zai zube, salkunan kuma za su lallace.
38 Men man skal komme ung Vin paa nye Læderflasker, saa blive de begge bevarede.
Amma dole ne a sa sabon ruwan inabi a sabobin salkuna.
39 Og ingen, som har drukket den gamle, vil have den unge; thi han siger: Den gamle er god.‟
Babu wanda zai yi marmarin sabon ruwan inabi bayan da ya sha tsohon, gama zai ce, “Tsohon ya fi sabon.”

< Lukas 5 >