< Salme 99 >

1 Herren regerer, Folkene bæve; han sidder over Keruber, Jorden ryster.
Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
2 Herren er stor i Zion, og han er ophøjet over alle Folkene.
Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
3 De skulle prise dit Navn som stort og forfærdeligt — hellig er han! —
Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
4 Og Kongens Vælde elsker Ret; du har befæstet Retvished, du har gjort Ret og Retfærdighed i Jakob.
Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
5 Ophøjer Herren vor Gud og tilbeder for hans Fødders Fodskammel — hellig er han! —
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
6 Mose og Aron iblandt hans Præster og Samuel iblandt dem, som paakaldte hans Navn, raabte til Herren, og han bønhørte dem.
Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
7 Han talte til dem i Skystøtten; de holdt hans Vidnesbyrd og den Skik, som han gav dem.
Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
8 Herre, vor Gud! du bønhørte dem, du var dem en Gud, som tilgav dem, men ogsaa en Hævner over deres Gerninger.
Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
9 Ophøjer Herren vor Gud og tilbeder for hans hellige Bjerg; thi hellig er Herren vor Gud.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.

< Salme 99 >