< Matthai 2 >

1 Manghai Herod tue vaengah Jesuh tah Judah ram Bethlehem ah thang, te vaengah khothoeng ben lamkah kholo hlangcueih rhoek Jerusalem la ha pawk uh.
Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
2 “Judah manghai aka thaang te melam a om? Anih kah aisi te khothoeng ben ah ka hmuh uh tih, anih bawk hamla ka pawk uh coeng,” a ti uh.
suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
3 Manghai Herod loh a yaak vaengah amah khaw, Jerusalem khaw boeih a hinghuen.
Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
4 Khosoihham rhoek neh pilnam khuikah cadaek rhoek te boeih a coi tih me kah Khrih nim aka thaang,” a ti nah.
Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
5 “Judea Bethlehem ah,” tila tonghma rhoek loh a daek te a a thui pa uh.
Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
6 “Judah ram kah Bethlehem nang ngawn tah Judah khoboei rhoek khuiah a yit la na om moenih. Nang lamloh hlang aka mawt ha thoeng ni. Anih loh ka pilnam Israel te a dawndah ni.
“‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
7 Herod loh kholo hlangcueih rhoek te a huep la a khue tih aisi a phoe tue te amih taengah a cae.
Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
8 Te phoeiah Bethlehem la a tueih tih, “Cet uh lamtah camoe kawng te khaeh khaeh dawt uh, na hmuh uh vaengah kai taengla, ha puen uh, te daengah ni ka lo vetih anih te ka bawk eh,” a ti nah.
Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
9 Manghai ol te a yaak uh nen tah vik cet uh. Te daengah khothoeng ah aisi te lawt a hmuh uh. Te dongah amih te camoe om nah a pha hil a lamhma pah tih a soah a pai pah.
Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
10 Aisi te a hmuh uh vaengah omngaihnah neh a nahla bahoeng omngaih uh.
Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
11 Im la a pha uh vaengah camoe neh a manu Mary te a hmuh uh dongah bakop doe ah a bawk uh. Te phoeiah a khohrhang te a ong uh tih a kutdoe la sui, hmueihtui neh myrrh te a paek uh.
Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
12 Tedae Herod taengah bal pawt ham a mang ah a mangthui pa tih a kho la a tloe longpuei longah bal uh.
Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
13 Amih a caeh uh phoeiah Boeipa kah puencawn loh Joseph mang ah pakcak phoe tih, “Thoo, camoe neh a manu te lo, Egypt la rhaelrham laeh, nang taengah kan thui hlan duela pahoi om laeh. Herod loh camoe te poci sak hamla cai tih a toem coeng,” a ti nah.
Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
14 Te dongah thoo tih camoe neh a manu te khoyin ah a loh tih, Egypt la cet.
Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
15 Te dongah Herod kah a dueknah rhi hil pahoi om. Te nen ni BOEIPA kah tonghma lamloh a thui tih, “Ka capa te Egypt lamkah ka khue,” a ti te a soep.
inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
16 Te vaengah Herod loh kholo hlangcueih kah a tamdaeng te a ming tih bahoeng a thinhul. A tue te kholo hlangcueih taeng lamloh a cae vanbangla Bethlehem khui neh a vaang pum khuikah hlang a tueih tih camoe kum nit hmui te boeih a ngawn.
Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
17 Te vaengah tonghma Jeremiah lamloh a thui tih,
Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
18 Rhama ah ol a yaak. Rhahnah neh nguekcoinah loh yet. Rakhel loh a ca rhoek te a rhah. Tedae a om uh voel pawt dongah a hloep te ngaih pawh,” a ti te soep.
“An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
19 Herod a duek phoeiah, Boeipa kah puencawn tah Egypt kah Joseph mang ah pakcak phoe tih,
Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
20 “Thoo, camoe neh a manu te lo lamtah Israel kho la cet laeh, camoe kah hinglu aka mae rhoek tah duek uh coeng,” a ti nah.
ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
21 Te dongah thoo tih camoe neh a manu te a khuen tih, Israel kho la a kun puei.
Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
22 Tedae Arkhelas loh a napa Herod yueng la Judea te a uk tila a yaak tih tela caeh ham a rhih. Te cakhaw mang ah a mangthui pah bangla Galilee pingpang la cet.
Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
23 Te phoeiah Nazareth la a khue khopuei la cet tih kho a sak. Te tlam ni tonghma rhoek lamloh, “Nazaren la a khue ni,” a ti te a soep eh.
ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”

< Matthai 2 >