< Johan 18 >

1 Jesuh loh hekah he a thui phoeiah a hnukbang rhoek neh Kidron sok rhalvangan la cet. Teah te dum pakhat om tih a hnukbang rhoek te a khuila a kun puei.
Bayan Yesu ya fadi wadannan maganganu, ya fita shi da almajiransa zuwa daya barayin kwarin Kidiron, inda wani lambu ya ke, ya kuma shiga da almajiransa.
2 Tekah hmuen ah a hnukbang rhoek neh Jesuh a humtun uh taitu dongah amah aka voei Judas long khaw a hmuen te a ming.
Yahuza ma wanda zai bashe shi ya san wurin, domin Yesu ya saba zuwa wurin da almajiransa.
3 Te dongah Judas loh caem a khuen hatah khosoihham neh Pharisee rhoek kah tueihyoeih rhoek long khaw hmaiim, hmaithoi, pumcumnah neh ha pawk uh.
Yahuza kuwa, bayan ya dauko kungiyar soja daga manyan firistoci, da Farisawa, da 'yan majalisa, suka zo wurin, rike da fitilu, da cociloli, da makamai.
4 Jesuh loh amah soah aka lo boeih te a ming dongah amih taengla cet tih, “Ulae na toem uh?” a ti nah.
Sai Yesu, da ya san duk abinda ke faruwa da shi, yayiwo gaba, yace masu, ''Wa kuke nema''
5 Amah te, “Nazareth Jesuh,” a ti nauh. Amih te khaw, “Kai ni he,” a ti nah. Te vaengah amah aka voei Judas khaw amih taengah pai.
Suka amsa masa su ka ce, ''Yesu Banazare'' Yesu yace masu, Ni ne'' Yahuza kuma, wanda ya bashe shi, yana tsaye tare da sojojin.
6 Te dongah amih te, “Kai ni,” a ti nah vaengah a hnuk la nong uh tih lai la bung uh.
Sa'adda ya ce masu, ''Ni ne'', suka koma da baya, suka fadi a kasa.
7 Te dongah amih te, “Ulae na toem uh,” tila koep a dawt. Te vaengah, “Nazareth Jesuh,” a ti uh.
Ya sake tambayarsu kuma, ''Wa ku ke nema?'' su ka ce, ''Yesu Banazare.''
8 Jesuh loh, “Kai ni tila nangmih taengah ka thui coeng. Te dongah kai ni nan toem uh atah hekah rhoek he hlah uh lamtah nong saeh,” a ti nah.
Yesu ya amsa, ''Ai, na gaya maku cewa, Ni ne. In kuwa ni ku ke nema, ku bar wadannan su tafi abinsu;''
9 Te daengah ni, “Amih te kai nan paek coeng dongah amih khuikah pakhat khaw ka hlong moenih,” tila a thui olka te soep eh.
Wannan kuwa domin maganar daya fada ta cika, ''Daga cikin wadanda ka ba ni, ko daya bai bace mani ba.''
10 Te vaengah Simon Peter loh a khueh cunghang te a yueh tih khosoihham kah sal te a boeng tih bantang hna te a hlueng pah Sal te a ming Malkhu ni.
Saminu Bitrus kuwa, da ya ke yana da takobi, ya zaro ya kai wa bawan babban firist sara, ya dauke masa kunnensa na dama, sunan bawan Malkus ne.
11 Tedae Jesuh loh Peter te, “Cunghang te capang khuila sang laeh. A pa loh kai m'paek boengloeng te ka o mahpawt nim,” a ti nah.
Yesu ya ce wa Bitrus, ''Mai da takobin ka kubenta. Ba zan sha kokon da Uba ya ba ni ba.'?
12 Te vaengah caem, rhalboeipa neh Judah rhoek kah tueihyoeih rhoek loh Jesuh te a tuuk uh tih a khih uh phoeiah Annas taengah lamhma la a khuen uh.
Sai sojojin da hafsan, da 'yan majalisar Yahudawa, suka kama Yesu, suka daure shi.
13 Anih te te vaeng kum kah khosoihham la aka om Kaiaphas kah a masae la om.
Da fari suka tafi da shi wurin Hanana, don shi surukin Kayafa ne, wanda ya ke shi ne babban firist a shekaran nan.
14 Te vaengah aka om Kaiaphas loh, “Hlang pakhat loh pilnam ham a duek te rhoei ngai, “tila Judah rhoek te a uen.
Kayafa kuma shi ne ya ba Yahudawa shawara, cewa ya fiye masu mutum daya ya mutu domin mutane.
15 Te vaengah Jesuh te Simon Peter neh hnukbang pakhat loh a vai. Tekah hnukbang te khaw khosoihham aka hmat la a om dongah Jesuh taengah khosoihham kah vongup la kun.
Saminu bitrus ya bi bayan Yesu, haka kuma wani almajirin yayi. Almajirin nan kuwa sananne ne ga babban firist, sai ya shiga har farfajiyar babban firist din tara da Yesu;
16 Tedae Peter tah thohka ah hoei pai. Te dongah khosoihham aka hmat hnukbang pakhat te cet tih imtawt nu te a voek phoeiah Peter te a khuen.
Amma bitrus kuwa ya tsaya a bakin kofa daga waje. Sai daya almajirin da ya ke sananne ga babban firist ya fita, yayi magana da macen da ta ke tsaron kofar, sa'an nan ya shigo da Bitrus.
17 Te dongah imtawt salnu loh Peter te, “Nang khaw hekah hlang kah hnukbang khuiah na om pawt nim?” a ti nah. Anih loh, “Ka om moenih,” a ti nah.
Sai yarinyar mai tsaron kofar ta ce wa Bitrus, ''kai ma ba kana cikin almajiran mutumin nan ba?'' Yace ''bani ba.''
18 Te vaengkah aka pai sal rhoek neh tueihyoeih rhoek loh khosik la a om dongah hmai a toih tih a om uh. Peter khaw om van tih amih aka pai rhoek taengah hmai a om.
To, barorin da dogaran Haikali suna tsaye a wurin, sun kuwa hura wutar gawayi, suna jin dumi, gama ana sanyi. Bitrus ma yana tsaye tare da su yana jin dumin.
19 Te vaengah khosoihham loh Jesuh te a hnukbang kawng neh a thuituennah kawng te a dawt.
babban firist ya tambayi Yesu game da almajiransa da koyarwarsa kuma.
20 Jesuh loh, “Kai loh Diklai taengah sayalh la ka thui coeng. Judah rhoek boeih a tingtun nah tunim neh bawkim ah ka thuituen taitu tih a huephael la ka thui moenih.
Yesu ya amsa masa, Ai, na yi wa duniya magana a bayyane. Na kuma sha koyarwa a majami'u da Haikali in da Yahudawa duka sukan taru. Ban fadi komai a boye ba.
21 Balae tih kai nan dawt? Ka thui te aka ya amih taengah dawt. Kai loh ka thui te amih loh a ming uh lahko,” a ti nah.
Don me kake tambaya ta? Ka tambayi wadanda suka saurare ni a kan abinda na fada, ai, sun san abinda na fada.
22 Tedae hekah he a thui vaengah aka pai tueihyoeih pakhat loh Jesuh te kutcaihnah la a khueh tih, “Khosoihham te na voek van pueng,” a ti nah.
Sa'adda Yesu ya fadi wannan, wani daga cikin 'yan majalisar da ke tsaye a wurin ya nushi Yesu, yace, ''Kana amsa wa babban firist haka.''
23 Jesuh loh anih te, A thae la ka cal atah a thae te han thui. Tedae a thuem atah balae tih kai nan boh,” a ti nah.
Yesu ya amsa masa yace, ''Idan na fadi mugun abu to, ka bada shaida kan hakan. In kuwa dai dai na fada, to, dan me za ka nushe ni?''
24 Te phoeiah Annas loh Jesuh te a khih tih khosoihham Kaiaphas taengla a thak.
Sai Hanana ya aika daYesu a daure wurin Kayafa, babban firist.
25 Te vaengah aka om Simon Peter khaw pai tih hmai a om. Te dongah anih te, “Nang khaw anih hnukbang rhoek khuikah la na om pawt nim? a ti nauh. Tedae anih te basa tih, “Ka om moenih,” a ti nah.
To Saminu Bitrus yana tsaye yana jin dumin. Mutanen kuwa suka ce masa, ''Anya kai ma ba cikin almajiransa ka ke ba?'' Sai yayi musu yace, ''A'a, ba na ciki.''
26 Khosoihham kah sal rhoek khuikah pakhat Peter loh a hna a hlueng pah te a huiko la om loh, “Kai loh anih neh nang te dum ah kan hmuh moenih a?” a ti nah.
Sai wani daga cikin bayin babban firist, wato dan'uwan wanda Bitrus ya fillewa kunne, yace, ''Ashe, ban gan ka tare da shi a lambun ba?
27 Tedae Peter koep a basa vaengah ai pahoi khong.
Bitrus ya sake yin musu, nan da nan kuwa zakara yayi cara.
28 Te phoeiah Jesuh te Kaiaphas taeng lamloh khoboeiyung la a khuen uh. Tedae a yue aih pueng dongah amih te khoboeiyung la kun uh pawh. Te daengah ni boi uh pawt vetih yoom te a vael mong eh.
Daga wurin Kayafa kuma suka kai Yesu fadar Gwamna. Da asuba ne kuwa, su kansu ba su shiga fadar Gwamnan ba, wai don kada su kazantu su kasa cin jibin Ketarewa.
29 Te dongah Pilat te poengla cet tih amih te, “Hekah hlang soah ba lai lae na pael uh,” a ti nah.
Sai bilatus fa ya fita zuwa wurinsu, yace, 'Wane zargi ku ke kawowa akan mutumin nan?'
30 Te vaengah anih a doo uh, “Anih loh a thae la a saii te om pawt koinih nang taengla anih kan thak uh mahpawh,” a ti uh.
''Sai suka amsa suka ce, ''idan da mutumin nan bai yi mugun abu ba, me zai sa mu yi kararsa a wurin ka''
31 Te dongah Pilat loh amih te, “Anih te namamih loh khuen uh lamtah namamih kah olkhueng bangla laitloek uh,” a ti nah. Judah rhoek loh, “Kaimih n'ngawn sak loengloeng moenih,” a ti uh.
bilatus yace masu, ''Ku tafi da shi da kan ku mana, ku hukunta shi bisa ga shari'arku!'' Sai Yahudawa su kace masa, ''Ai, ba mu da ikon zartar da hukuncin kisa akan kowa.''
32 Te daengah ni Jesuh kah olka loh, 'Duek ham cai tih dueknah te a phoe,’ a ti te a soep eh.
Sun fadi Wannan ne don a cika maganar da Yesu yayi, wadda ta kwatanta irin mutuwar da zai yi.
33 Te phoeiah Pilat te khoboeiyung la koep kun tih Jesuh te a khue phoeiah, “Nang he Judah manghaila na om a?” a ti nah.
Sai bilatus ya sake shiga cikin fadar Gwamnan, ya kira Yesu ya ce masa, ''kai sarkin Yahudawa ne?''
34 Jesuh loh, “Hekah he nang loh namah lamkah nim na thui? A tloe rhoek loh nang taengah kai kawng han thui a?” a ti nah.
Yesu ya amsa, '' wannan fadarka ce, ko kuwa wadansu ne suka ce da ni haka a wurinka?''
35 Pilat loh, “Kai he Judah hlang la ka om ngawn pawh. Balae na saii tih na namtu neh khosoihham rhoek loh kai taengla nang n'thak?” a ti nah.
Bilatus ya amsa “Ni ba Bayahude bane, ko kuwa?'' Ai, jama'arka ne da manyan firistoci suka bashe ka gareni. ''Me ka yi?''
36 Jesuh loh, “Kai kah ram tah he Diklai kah ram la om pawh. Kai kah ram tah he Diklai kah ram la om koinih Judah rhoek te kai m'voeih pawt ham ka tueihyoeih rhoek loh a hnueih uh ni. Tedae kai kah ram te heah om pawh,” a ti nah.
Yesu ya amsa, ''Mulkina ba na duniya nan ba ne. Da mulkina na duniyan nan ne da barorina za su yi yaki kada a bashe ni ga Yahudawa. To, mulkina ba daga nan ya ke ba.''
37 Te dongah Pilat loh, “Te koinih nang manghai la na om a?” a ti nah. Jesuh loh, “Manghai la ka om te namah long ni na thui. Oltak phong ham kai ka thaang tih he ham ni Diklai la ka pawk. Oltak kah hlang la aka om boeih loh kai ol a hnatun,” a ti nah.
Sai Bilatus yace masa, ''Wato ashe, sarki ne kai?'' Yesu ya amsa, ''Yadda ka fada, ni sarki ne. Domin wannan dalili aka haife ni, domin kuma wannan dalili na zo cikin duniya, don in bada shaida game da gaskiya. Kowane mai kaunar gaskiya kuma yakan saurari muryata.''
38 Pilat loh, “Oltak te ba lae?” a ti nah. Hekah he a thui phoeiah Judah rhoek taengla koep cet tih amamih te, “Anih dongah paelnaehnah ka hmuh moenih.
Bilatus yace masa, ''Menene gaskiya?'' Bayan da ya fadi haka, ya sake fitowa wurin Yahudawa, yace masu, ''Ni kam, ban sami mutumin nan da wani laifi ba.
39 Tedae yoom ah nangmih taengkah pakhat ka hlah ham namamih khosing om. Te dongah Judah manghai te hlah ham nangmih na ngaih uh a?” a ti nah.
Amma dai kuna da wata al'ada, in Idin Ketarewa ya yi, na kan sakar maku mutum daya. To, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?''
40 Te dongah koep pang uh tih, “Anih moenih Barabbas te,” a ti uh. Te vaengah Barabbas tah dingca la om.
Sai suka sake daukar kururuwa suna cewa, ''A; a, ba wannan mutum ba, sai dai Barabbas.'' Barabbas din nan kuwa dan fashi ne.

< Johan 18 >