< Joba 37 >

1 He dongah ka lungbuei lakueng tih a hmuen lamloh cungpet.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 A ol dongkah khoponah te hnatun rhoela hnatun. A ka lamloh caitawknah thoeng.
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Vaan boeih hmuiah a hlah tih a vangnah loh diklai hmoi duela pawk.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 A hnukkah a kawk ol khaw a hoemdamnah ol neh hum tih, a ol a yaak vaengah rhaek uelh sak boeh.
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Pathen loh a ol neh khobaerhambae a saii khungdaeng tih, hum dae m'ming uh moenih.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Vuelsong neh khotlan khonal te, ‘Diklai ah om saeh,’ a ti vaengah khotlan khonal khaw a sarhi tak.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Amah kutngo hlang boeih ming sak ham hlang boeih kah kut te rhodaek a soei pah.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 Te vaengah mulhing khaw a khui la kun tih a khuisaek ah kho a sak.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 Cangpalam te imkhui lamloh, khosik te tlangpuei lamloh ha thoeng.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Pathen kah hiil lamloh rhaelnu khaw a khueh tih tui daang mangdaeng mangtok la om.
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 Khomai te cingtui loh a rhih sak tih, cingmai loh amah kah vangnah te a taekyak.
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 Te khaw diklai kah lunglai hman ah a uen boeih te saii hamla a niing, a niing dongah kuluk la a hil.
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 Te te caitueng lam khaw, a khohmuen ham khaw, sitlohnah ham khaw a thoeng sak.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 Job, he he hnakaeng lah. Pai lamtah Pathen kah khobaerhambae he yakming lah.
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 Te rhoek soah Pathen loh a khueh tih a cingmai kah vangnah a sae te na ming a?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Poeknah rhuemtuet, mangvawt khomai a haainah te na ming a?
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 Tuithim loh khohmuen a mong sak vaengah na himbai te aka bae sak,
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 Hmaidan a hlawn bangla khomong a thah la amah taengah na nulh thai aya?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Amah taengah metla n'thui ham khaw kaimih n'tueng lah. Hmaisuep hmai ah n'tawn uh thai pawt oe.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Hlang loh a dolh hamla thui cakhaw ka thui bangla amah taengah a tae pa aya?
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 Tahae ah khaw vangnah a hmuh uh moenih. A aa te khohli loh a yawn tih, a caihcil hnukkah khomong dongah tueng.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Tlangpuei lamkah sui te mueithennah rhih om Pathen taengla pawk.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 Tlungthang te thadueng a len dongah a tiktamnah m'hmuh lek moenih. Duengnah khaw a cungkuem dongah hlang a phaep moenih.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Hlang rhoek loh amah te a rhih uh tangloeng dongah lungbuei aka cueih rhoek takuem khaw a sawt moenih,” a ti.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”

< Joba 37 >