< Исая 21 >
1 Наложеното за пустинята на морето пророчество: Както южните вихрушки, които стремително летят, Така иде разрушение от пустинята, от страшната земя.
Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
2 Тежко видение ми се откри: Коварният коварствува, и грабителят граби. Възлез, Еламе; обсади, Мидийо; Спрях всичките й въздишания.
An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
3 Затова хълбоците ми са пълни с болеж; Болки ме обзеха като болките на жена, когато ражда; Сгърбен съм та не мога да чуя, Смутен съм та не мога да видя.
Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
4 Сърцето ми се разколебава, трепет ме ужаси; Дрезгавината, която пожелах, се обърна на страшилище за мене.
Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
5 Приготвят трапезата, поставят стражата, ядат, пият! Станете, военачалници! излъскайте щитове!
Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
6 Защото Господ ми рече така: Иди постави страж, Та нека възвестява каквото види.
Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
7 И видя полк конници по двама, Полк осли, и полк камили; Тогава вникна добре с голямо внимание.
Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
8 После, извика като лъв: Господи, аз стоя непрекъснато в стражарницата през деня, И оставам в стражата си целите нощи.
Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
9 Но, ето! иде тук полк мъже, конници по двама! И той проговарайки рече: Падна, падна Вавилон, И всичките изваяни идоли на боговете му се строшиха на земята!
Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
10 Врахо мой, и ти произведение на гумното ми, Явих ви онова, което чух от Господа на Силите, Израилевия Бог.
Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
11 Наложеното за Едом пророчество: Към мене вика един от Сиир: Стражо, колко е часът на нощта? Стражо, колко е часът на нощта?
Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
12 Стражът рече: Утрото иде, още и нощта; Ако искате да питате, питайте; дойдете пак, дойдете.
Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
13 Наложеното за Арабия пророчество: Привечер ще слезете в гората да пренощувате. О дедански кервани.
Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
14 Жителите на теманската земя Донесоха вода за жадния, Посрещнаха бежанците с хляба си.
ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
15 Защото побягнаха от сабите, От оголената сабя, от запънатия лък, И от лютостта на войната.
Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
16 Защото Господ ми рече така: Вътре в една година, каквито са годините на наемник, Ще изчезне всичката слава на Кидар;
Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
17 И останалото число на стрелците, Силните мъже на кидарците, ще бъде малко; Защото Господ Израилевият Бог е изговорил това.
Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.