< Ndu Manzaniba 20 >

1 Niwa gro wu a kle'a, Bulus a ton ba ka yo mri ko bi hu'a nda nron ba du ba ki gbangban, nda tre ndi duba mla ki nda kuunko hi ni Macedonia.
Bayan da rikici ya kare, Bulus ya aika a kira al'majiran, ya karfafa su. Sa'annan ya yi bankwana da su, ya tashi zai tafi Makidoniya.
2 Niwa a zren zu ni gbungblu bi koki nda gbre ba ni lantre gbugbuwu, a ye rini Greece.
Bayan ya ratsa cikin lardunan yana yi wa masu bi gargadi sosai, sai ya zo kasar Helenawa.
3 Hu gon kima a son ti wha tre niki. Yahudawa ba ba mla nkon meme ti nitu ma, niwa a ta dran hun koma hi ni Syria; nitu ki a kma sran ka zu ni Macedonia.
Sa'adda ya yi wata uku a wurin, Yahudawa suka kulla masa makirci, yayin da yake shirin hawa Jirgi zuwa Suriya, sai ya canza ra'ayi ya koma ta Makidoniya.
4 Kpan zren ma ba wa baka rini Asia, bana sopater ivren Pyrrhus wa a rhini Berea, Aristakus mba Sekondus, hamba bana bi Tasalonika wa ba kpanyime, Gaius wu Derbe, Timoti, mba Tychicus mba Trophimus wa a rhi ni Asia.
Masu yi wa Bulus rakiyar zuwa yankin Asiya sun hada da Sobatarus dan Burus daga Biriya; Gayus mutumin Derbe; Timoti da Aristakus da Sakundus, dukansu masu bi ne daga Tasalonika; da Tikikus da Trofimus daga Asiya.
5 Ndji biyi bana guchi hi nitawu nda ka sia gbenta ni Troas.
Amma wadansu har suka rigaye mu, suka jira mu a Taruwasa.
6 Ki dran rhuni Philippi niwa ivi bi bredi wa ana fuulu, a kle, mba ni vi u ton ki ye tsra niba ni Troas. Niki ki son u vi tangban.
Da muka shiga Jirgi daga Filibi bayan kwanakin Gurasa mara yisti; bayan kwanaki biyar muka iske su a Taruwasa; kwananmu bakwai a wurin.
7 Ni vi mumla u Sati ki, niwa kina zontu niki nzi bredi, Bulus a tre ni biwa ba kpanyime'a. A ta son don ba ni viwu hu kima, nitu ki a tre gbron nkon hi ni tsutsuchu.
A rana ta fari ga mako, da muka taru domin karya gurasa. Bulus ya yi wa masubi jawabi, don ya yi niyyar ya tafi da wayewar gari; jawabinsa ya kai har tsakar dare.
8 Ilu fitila gbugbuu bana he ni tra u koshu, bubu wa kina zontu ki.
A benen da suka taru akwai fitilu da yawa.
9 Ni windo'a, vren nze ri ni nde Eutychus a son, e inna a kri koonvu. Niwa bulus a tre la gbron nkon nha, vren nze yi, wa a risi kruna, a kurjoku rjini tuko u tra i baka baun kmomu.
Wani matashi mai suna Aftikos yana zaune a kan taga, barci mai nauyi ya dauke shi; da shike Bulus ya tsawaita jawabinsa, saurayin da shike barci mai nauyi ya dauke shi sai ya fado daga kan bene na uku aka dauke shi matacce.
10 Bulus a grji hi, kukru tsra kpama nituma nda maanji ye ni kpama. Mle nda tre, “Du sron mbi na ti meme zan toyi na, a he ni sisren.”
Sai Bulus ya sauka ya mike a bisansa ya rungume shi, sa'annan ya ce, “Kada kowa ya damu; domin yana darai bai mutu ba.”
11 Niki a kma hon hi ni tra u koshu'a nda ka nzi bredi tan. Hu gon wa ala si tre ni ba wu gbro nton ka tsra ni bwu mble, a rju kaba don.
Sa'annan ya hawo kan bene domin cin gurasa tare da su, ya yi magana da su har gari ya waye daga nan ya bar su.
12 Ba nji vren nze'a kma ye ni sisren ma e sron mba a kusi.
Suka kawo saurayin da rai, sun sami ta'aziya ba kadan ba.
13 Kita ngame ki zren guchi ni Bulus nitu jirgi ma, ki dran hi ni Assos, bubu wa kina banzi ki ban Bulus yonji nita. Ana toki me wawu kima ana son ti, nitu ana ya ndi ani hu nkon u meme hi.
Amma mu, da muka riga Bulus zuwa gun Jirgin, muka shiga zuwa Asos, mun shirya mu dauki Bulus a jirgi amma shi ya kudurta ya yi tafiya a kasa.
14 Niwa a zontu nita ni Assos, ki baun yo ni mi jirgi'a ni hi ni Mitylene.
Da muka sadu a Asos, mun dauke shi a Jirgin ruwa zuwa Mitilitus.
15 Niki ki dran rhini kima ka ri ni vi wa aka hua, ni bubu wa ata ya nklan meme wu Chios. Ni vi wa ala hu'a, kika yo za ni nklan meme wu Samos, e vi wa aka hu kima, ki ye ri ni kikle gbu Miletus.
Bayan tashin mu daga can, washegari muka zo tsibirin Kiyos. Washegari kuma muka zo birnin Militus.
16 Nitu Bulus ana banzi ndi ani dran vu Ephesus yba, nitu du wawu na wo nton ni Asia na; a ta sima hi ri ni Urushelima nitu hi tsra ni vi Pentecost, anita bi tiwu toki.
Amma Bulus ya kudurta wucewa Afisa a Jirgi, don kada ya bata lokaci a Asiya, don yana sauri in ya yiwu ranar Fentekos ta same shi a Urushalima.
17 Rjini Miletus a ton ndji hi ni Ephesus duba ka yo bi ninkon ekklisiya ye wu.
Daga Militus ya aika a kira masa dattawan iklisiyar Afisa.
18 Niwa ba ye'a, a hla bawu ndi, “Bi yi kimbi bito, rhini vi mumla wa mi yo za ni Asia, niwa chachu mi zi wunton niyi.
Da suka zo wurinsa sai ya ce masu, “Ku da kanku kun san tun daga ranar da na sa kafata a Asiya, irin zaman da muka yi da kasancewar mu tare.
19 Mi zi ti ndu Bachi hama ni nzutu mba ni Mashishi, mba ni tsra iya wa ye ni me nitu zon nyu meme wu Yahudawa ba.
Na bauta wa Ubangiji da tawaliu har da hawaye, da wahalun da na sha saboda makircin Yahudawa.
20 Bito nitu wa mi na kamu ni dbu bla ni yiwu ko ngye wa ani zoyi na, mba wa mi tsro yi ni shishi ndji wawu mba huyi niko niko,
Kun sani ban ji nauyin sanar da ku kowanne abu mai amfani ba, na bi ku gida gida ina koyar da ku abubuwa a sarari.
21 ni ni vu ni nran ni Yahudawa baba bi Greek nitu kma sron hi ni Irji mba kri ni gbangban sron ni Bachi mbu Yesu.
Kunsan yadda na gargadi Yahudawa da Hellenawa game da tuba ga Allah da bangaskiya ga Ubangiji Yesu.
22 Zizan ya, mi si hi ni Urushelima, ni gbron Ruhu, nina to kpe wa ani ti nimu niki na,
Yanzu fa, gashi, zan tafi Urushalima, Ruhu Mai Tsarki ya nuna mani a fili dole in je, ban san abin da zai faru da ni a can ba.
23 hamma wa Ruhu Tsatsra a bwu bla nimu ndi ni gbu kankan wa mi ria, wlo cbo wu lo mba iya ni gben me.
Sai dai Ruhu Mai Tsarki ya nuna mani a kowanne gari cewa, sarkoki da wahalu suna jira na.
24 E me mina ban kpa ivri sisren mu to hi kpe wu tumu na, nitu du mi kle itsu mba ndu wa mi kpa rjini Bachi Yesu, ni du mi bwu nran tre ndindi wa Irji nme wo kpata hama duta ki han kpe.
Amma ban dauka cewa raina yana da wani amfani gare ni ba, domin in cika tsere da hidimar da na karba daga wurin Ubangiji Yesu, ta shaidar bisharan alherin Allah.
25 Zizan ya, Mito ndi wawu mbi, wa nimi mbi mi zren si dbu hla nitu ikoson Irji, bina la to shishi mu na.
Yanzu fa, duba, na san dukanku, wadanda na yi wa wa'azin mulkin Allah, ba za ku kara gani na ba.
26 Nitu kima, mi bwu ni bla yiwu vi wu luwa iyi ndrjo na he ni tumu na.
Don haka na shaida maku a wannan rana, ba ni da alhakin jinin kowanne mutum.
27 Nitu mina ka kpe don ni dbu bla wawu kpe wa Irji ni son niyi na.
Don banji nauyin sanar maku da dukan nufin Allah a gare ku ba.
28 Nitu kima, bika mla zren ni kpambi, mba ni ba wawu ntma wa Ruhu Tsatsra a yoyi du yi yaba niwu'a. Mla zren ni krju ekklisiya Irji, wa a le ba ni iyi ma. / Nitu du he ndi / ni iyi ma / nha vunvu bi sen bari ba yo ndi / ni iyi wu vren ma
Saboda haka ku kula da kanku, da masubi da Ruhu Mai Tsarki ya sanya ku shugabanni. Ku kula ku yi kiwon iklisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa.
29 Mi toh ndi, mita hi kpamu, meme yawhu bari ni mi mbi ba ye nda na kpa ntma ba chuwo na.
Na sani cewa bayan tafiyata, kyarketai masu zafi za su shiga tsakaninku, kuma baza su rangwanta wa masubi ba.
30 Mi to ndi nimi mbi me, ndji bari ba nzulu nda tre kpe bi gbran rhen nitu du ba gbron mriko bihu bari hi ni kpan mba.
Na sani har daga cikinku wadansu mazaje za su zo su fadi gurbattatun zantattuka, domin su janye almajirai zuwa gare su.
31 Nitu ki bika mla kri. Bika ti mren ndi wu se tra mina don me ni nron yi yiyyri mbi ni mashishi ni chu mba ni irhi.
Saboda haka ku yi lura. Ku tuna da cewa shekara uku ban fasa yi wa kowannenku gargadi da hawaye dare da rana ba.
32 Zizan mi yoyi ni wo Irji mba ni lan tre u wa a kpata, wandi ani to me yi nda nuyi gado nimi biwa ba ngla ba ti tsatsra'a.
Yanzu ina mika ku ga Allah, da maganar Alherinsa, wadda take da ikon gina ku ta kuma ba ku gado tare da dukan wadanda ke cikin kebabbu na Allah.
33 Mina ti ngu yo sron nitu azurfa, zinariya ko nklon ndrjo na.
Ban yi kyashin azurfa, ko zinariya, ko tufafin wani ba.
34 Biyi me bi to ndi iwo mu biyi ba tindu ne kpiwa mi son mba kpison wu bi wa ba he ni me'a.
Ku da kanku kun sani na yi aiki da hannuwana, na biya bukatu na da na wadanda ke tare da ni.
35 Ni kpi wawuu, mi bwu nkon tsro yi nitu wa bi zo bi wa bana he ni gbengblen na, ni tindu, mba niwa bi timre ni lantre Bachi Yesu, lan tre wa wawu kima a tre: A zan bi lulu du hu nu ni du hu kpa,”
Na zama maku abin koyi a kowace hanya game da yadda za ku taimaka wa nakasassu ta wurin aiki, da yadda za ku tuna da maganar Ubangiji Yesu, maganar da shi da kansa ya ce: ''Bayarwa tafi karba albarka.''
36 Hu gon tre ma ni nkon yi, a kukwu mgbarju nda bre Irji ni ba wawu mba.
Bayan da ya yi magana haka, ya durkusa ya yi addu'a tare da su duka.
37 Ba kuuyi bran nda mankpa Bulus nji nda chiwu bi bi wu sron nyime.
Dukansu kuwa suka yi kuka mai tsannani, suka rungume shi kuma suka sunbace shi.
38 Sron mba a ti meme zan nitu wa a tre ndi bana la to shishima ngana. Mle ba huu ka yo ni nkon ni jirgi ma'a.
Suka yi bakin ciki musamman domin abin da ya ce masu, ba za su kara ganinsa ba. Sai dukansu suka yi masa rakiya zuwa wurin jirgin ruwa.

< Ndu Manzaniba 20 >