< Romawa 1 >
1 Bulus vren koh Yesu Almasihu, wa ba you aye, kma tie ndji u toh ndu, wa ba chu zi kan nitu tre Irji.
Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah.
2 Wa i hi tre wa a chu nyu ni sen mu ni bi toh ndu ma ni tsatsraka ibe ma.
Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa.
3 Ahe ni tu vren ma, wa ba ngrji'u ni kutra kahlan Dauda ni kpa.
Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.
4 Ni Brji ndindima u suron ndindi, wa a lunde ni mi be bak tsro da Vren Irji ni gbengblen Ibrji ndindi u bi wa ba he kiklan suron u Yesu Almasihu Bachi mbu
Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu.
5 Ni tuma ki kpa ndindi ni toh ndu nitu kpa nyime u ndindi nimi bi korah wawu'u, nitu inde ma u ndindi.
Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa.
6 Ni mi bi kora kwa, bi yi me ba you yi hi ni Yesu Almasihu.
cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.
7 Lbe i ahi u bi wawu'u bi wa bi he ni mi Roman, wa Irji ni son ba, wa ba you ndji mba ndi tsarkaku. Du ndindi ni sun si rji ni Irji Bachi Iti mbu, ni Bachi Yesu Almasihu.
Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
8 Ikpe u mumla misi ngyiri ni Irji mu ni tu Yesu Almasihu nitu bi wawu'u, don naki basi tre nitu njanji bi ni gbungblu wawu'u.
Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya.
9 Don Irji wawu yi toh me, wa misi tie ndu ma ni mi Ruhu mu ni tre Vren Ma, wa mi you nde bi chachu'u.
Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku.
10 Mi nji yi mu ni bre chachu'u du me toh koh wa mi ye u Hellinawa.
A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.
11 Nakima Irji na hi u tara na.
Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku.
12 Ni biwa ba lah tre ni tron na, ba kwu ba tare da tron na, ni bi wa ba lah tre ni mi tron, ba hukunta ba nitu tron.
Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.
13 Naki ma ana biwa ba wo tron, ana baba bi ndindi u Irji na, naki bi ti, ba kpa ba chuwo.
Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai.
14 Bi kora wa bana toh tron na, nitu da bia bati kpi wa ahi u tron.
Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima.
15 Nakima ba tsro ndi idu ni tron ani wa han ni suron ba, imre ba ni bla, ri mre ba ni chan ba ko ani ka'aba. Nakima ni Irji wa i ni ti ni vie wa Irji ni bla asiri wa he riri u bi he ni mi Roma
Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.
16 Nakima isha na time na, dume hla tre na, don kima hi gbengblen Irji don kpachuwo wa bi wa ba kpa nyime, bi mumla Yahudawa u Halleniyawa.
Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,
17 Naki nimi ma ndindi Irji ka tsro u njanji hi ni njanji, na ba nha zi, ndji u ndindi ani sun nitu njanji.
Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, “Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya.”
18 Nakima infu Irji a tsro rji ni shu nitu bi wa bana hu nkon ni ndindi u mri Adamu bi wa ba chan njanji nitu njanji na he ni bana.
Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su.
19 Nakima, ikpe wa a mla duba toh ni Irji ahe ni rira me nitu mba Naki ma Irji a tsro ba wawu hi zahiri.
Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.
20 Nakima idu ma wa bana ya toh na a ni rira ba he tu ni nton wa ati gbungblu'a. Ba ya toh ba nitu ikpi bi wa ati'a. Ikpi bi yi baba ba ikoma u kakle ni Allahtakarsa. Nakima indji bi bana he ni sen nyu na. (aïdios )
Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. (aïdios )
21 Nakima ba ndji ba toh Irji, aman bana no ninkon u matsayi Irji na, ko duba tsro ingyiri. Nakima ba kma ti ruru ni mi mre mba. Imre u suron mba hi u bu.
Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.
22 Ba ban tumba na bi wa ba toh, aman se ba kma tie ruru.
Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye.
23 Ba sran ninkon Irji u kakle ni kpi wa bana kakle ana na indji, cicen ni na nma bi zizia ni biwa ba nha ni ne.
Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.
24 Nakima Irji ka ban no sha'awa pipi suron mba ba ti kpa yah.
Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu.
25 Baba yi ba sran njanji Irji ni che, ba si tie sujada ni bauta ni kpe wa ba tie ba ni wo, maimako wa ati ta, wa a mla zu nde kakle. (aiōn )
Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin. (aiōn )
26 Nakima Irji ban ba no sha'awoyi u ti fa ba iyah har mbah ba kasran kaida jima hi mbah ni mbah.
Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace.
27 Lilon ba bame ba sran kaida jimai u lilon ni mbah hi ni lilon ni lilon ba si tie ndu fa. Lilon ba kru ni lilon nda ni tie kpi u chi basi chan sakamako indu mba u chi.
Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.
28 Nakima bana kpa nyime ni Irji na ni mi duba, Irji ban ba no ni kpa risu ni mre mba, basi tie meme kpi biyi.
Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.
29 Ba shu ni rashi ndindi, meme kyashi, keta, tigu, wudi, wa-nyu, makirci, ni meme mre.
Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi.
30 Bi ti pre, kage, bi wa bana son Irji na. Bi wa bana son sun si na, bi santu, ni bi gla, bi ha meme che, ni bi wa bana hu/wo ba ti/yi mba.
Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu.
31 Biwa isuron mba tsro pipi me, biri amana biwa bana he ni son na, bi wa bana he ni lo suron na.
Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.
32 Ba toh tsari Irji tre bi wa bati ikpi baki, ba mla kwu, ana ti kpi ni kangrji na, hra ba hu gon biwa bati ba.
Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.