< Asunasi Dunu Ilia Hou 25 >

1 Fesadase da Sesaliaga doaga: le, eso udiana aligili, yolesili asili, Yelusaleme moilai bai bagade amoga doaga: i.
Da Festas ya shiga lardin, kuma bayan kwana uku, ya tashi daga Kaisariya ya tafi Urushalima.
2 Yelusalemega, gobele salasu ouligisu dunu amola Yu ouligisu dunu da Boloma fofada: su liligi ema olelei.
Sai babban firist da manyan Yahudawa suka kawo wa Festas sara a kan Bulus.
3 Ilia Fesadasema e da Bolo Yelusaleme moilai bai bagade amoga fofada: musa: oule misa: ne, ha: giwane sia: i. Bai ilia da logoga Bolo medole legemusa: ilegeiba: le, amane sia: i.
Suka roki tagomashi wurin Festas ya kira Bulus zuwa Urushalima domin su kashe shi a hanya.
4 Be Fesadase da bu adole i, “Bolo da Sesalia se dabe iasu diasu ganodini sali esala. Na da fonobahadi aligili, Sesalia moilaiga buhagimu.
Amma Festas ya amsa masu cewa, Bulus dan sarka ne a Kaisariya, kuma ba da dadewa ba shi da kansa zai koma can.
5 Dilia ouligisu dunu da Sesalia moilaiga na sigi asili, Bolo da wadela: i hou hamoi galea, ema fofada: mu da defea.”
“Saboda haka duk wadanda za su iya, su biyo mu. Idan akwai wani laifi game da mutumin, sai ku zarge shi.”
6 Fesadase da eso nabuane Yelusaleme moilai bai bagadega ouesalu, Sesalia moilai amoga asi. Golale hahabe, e da fofada: su diasuga golili sa: ili, fili, Bolo ema oule misa: ne sia: i.
Bayan kwana takwas ko goma, sai ya gangara zuwa Kaisariya. Washegari ya zauna bisa kursiyin shari'a ya bada umarni a kawo Bulus a gabansa.
7 Bolo da doaga: loba, Yu dunu amo da Yelusalemega misi ilia da Boloma bagadewane diwaneya udidili sia: nanu. Be ba: su dunu hameba: le, Bolo dafamu da hamedei ba: i.
Da Bulus ya iso, Yahudawa daga Urushalima suka tsaya kusa, suka yi ta kawo kararraki, amma basu iya tabbatar da su ba.
8 Bolo da ea hou gaga: i, amane, “Na da ninia Sema, Yu dunu, Debolo Diasu amola Louma gamane ouligisudafa, amo huluanema wadela: le hamedafa hamoi.”
Bulus ya kare kansa ya ce, “Ban yi wa kowa laifi ba, ko Yahudawa, ko haikali, ko kuma Kaisar.”
9 Be Fesadase da Yu dunu na: iyado hamomusa: dawa: beba: le, e da Boloma amane adole ba: i, “Di da Yelusaleme moilai bai bagade amoga amo fofada: su hou nama bu fofada: ma: ne masunu da defeala: ?”
Amma Festas yana neman farin jini wajen Yahudawa, sabo da haka ya tambayi Bulus ya ce, “Kana so ka je Urushalima in shari'anta ka a can game da wadannan abubuwa?”
10 Bolo da bu adole i, “Na da Louma gamane ouligisudafa amo ea fofada: su diasudafa amo ganodini lela. Amo da defea. Na da Yu dunu wadela: ma: ne, wadela: i hamedafa hamoi. Amo di noga: le dawa:
Bulus ya ce, “Ina tsaye a Ddakalin Shari'ar Kaisar inda dole a shari'anta ni. Ban yi wa Yahudawa laifi ba, kamar yadda ka sani sosai.
11 Na da Sema wadela: lesi ganiaba, o se imunusa: fofada: su amo defele wadela: i hamoi ganiaba, na da se imunusa: fofada: mu da defea gala: loba. Be nama fofada: su da ogogoi ganiaba, na da se imunusa: fofada: mu da defea hame gala: loba. Na da Louma gamane ouligisudafa ema fofada: ma: mu.”
Idan lallai na yi laifi kuma na yi abin da ya chanchanci mutuwa, ban ki ba in mutu. Amma idan zarginsu karya ne, kada kowa ya bashe ni gare su. Ina daukaka kara zuwa ga Kaisar.”
12 Amalalu, Fesadase, ea fada: i adole iasu dunuma gilisili sia: dalu, Boloma bu adole i, “Di da Louma Gamane ouligisudafa ema fofada: musa: adole ba: beba: le, defea, di da ema fofada: musa: masunu!”
Bayan Festas ya tattauna da majalisa ya amsa ya ce, “Kana kira ga Kaisar; za ka tafi wurin Kaisar.”
13 Fa: no, hina bagade Agaliba amola idua Benisi, da Fesadase gousa: musa: , Sesalia moilaiga misi.
Bayan wadansu kwanaki, sarki Agaribas da Barniki suka iso Kaisariya domin su ziyarci Festas.
14 Eso udianawane esalu, Fesadase da Agalibama Bolo ea hou olelei, amane, “Dunu da guiguda: esala, Filigisi da asiba: le, amo e da se dabe iasu diasu ganodini sali amomane fisi.
Da ya kasance kwanaki da yawa, Festas ya fada wa sarki labarin Bulus ya ce, “Akwai wani mutum dan sarka da Filikus ya bari a kurkuku.
15 Na da Yelusaleme moilai bai bagade amoga asili, Yu gobele salasu ouligisu dunu amola asigilai dunu, ilia da e da wadela: le hamoi amo sia: i. Ilia da na ema medoma: ne fofada: musa: sia: i.
Sa'anda nake a Urushalima, babban firist da dattawan Yahudawa suka kawo kararsa gare ni, suka roka a kashe shi.
16 Be na ilima bu adole i, ‘Ninia Louma dunu hou da agoane gala. Dunu ilia eno dunu da wadela: le hamoi sia: beba: le, ninia da amo dunuma udigili hame fofada: sa. E da ea hou gaga: ma: ne, ema fofada: su dunu hidadea ilia odagi ba: beba: le fawane fofada: mu!’ na amane sia: i.
Game da wannan na amsa na ce masu, ba al'adar Romawa ba ce a ba da mutum tagomashi; sai wanda ake kararsa an bashi zarafi ya kare kansa a gaban masu kararsa, ya kuma bada hujjojinsa game da kararakin.
17 Amaiba: le, ilia guiguda: manoba, golale hahabe na da hedolowane fofada: su diasu amo ganodini fili, na dadi gagui ilima Bolo ganodini oule misa: ne sia: i.
Saboda haka, da duk suka taru ban bata lokaci ba, washegari na zauna a kujerar shari'a, na ba da umarni a kawo mutumin.
18 Ema ha lai dunu da wa: legadole, ema diwaneya udidi. Na da agoane dawa: i galu. Ilia da e da wadela: idafa hou hamoi sia: mu na dawa: i galu. Be hame.
Da masu karar suka fadi kararsu, sai na fahimci karar ba wani muhimmin abu a cikinta.
19 Be ilia ema amane fofada: i. E da ilia Gode Ea sema wadela: lesi, ilia sia: i. Amola e da ogogosu dunu ea dio amo Yesu da bogoi be bu wa: legadole esala, amo ogogole sia: i, ilia diwaneya udidi.
Sai dai na ga cewa jayayya ce tsakanin su ta addini a kan wani Yesu da ya mutu, wanda Bulus ya ce yana da rai.
20 Na da amo hou bai dawa: mu gogolei galu. Amaiba: le, Boloma na amane adole ba: i, ‘Di da Yelusaleme moilai bai bagade amoga amo fofada: su hou bu fofada: ma: ne masunu da defeala: ?’
Na rasa yadda zan bincike wannan al'amarin, sai na tambaye shi ko zai je Urushalima a shari'anta shi kan wadannan abubuwa.
21 Be Bolo da Louma gamane ouligisudafa ema fofada: musa: sia: i. E da se dabe iasu diasu sosodo aligisu dunu amoga ouligilalu, Louma gamane ouligisudafa fofada: musa: masunu sia: i. Amaiba: le, na dadi gagui dunuma, na amo hou hamomusa: sia: i. Na da Louma gamane ouligisudafa ema asunasimusa: dawa: i!”
Amma da Bulus ya nemi a lura da shi, Kaisar ya shari'anta shi, sai na ba da umarni a ajiye shi har sai na aika shi wurin Kaisar.”
22 Agaliba da Fesadasema amane sia: i, “Amo dunu ea sia: nisu nabimu hanai gala.” Fesadase da bu adole i, “Defea! Aya hahabe di da nabimu!”
Agaribas yace wa Festas. “Zan so ni ma in saurari mutumin nan.” “Gobe za ka ji shi,” in ji Fostus.
23 Golale hahabe, Agaliba amola Benisi da misini, dunu bagohame elama nodone hamonanebe ba: i. Dunu gilisisu diasu bagade amo ganodini golili sa: ili, dadi gagui ouligisu dunu huluane amola moilai ouligisu dunu, gilisila misi. Fesadase sia: beba: le, sosodo aligisu dunu da Bolo diasu ganodini oule misi.
Washegari Agaribas da Barniki suka zo tare da kasaitaccen taro suka shiga dakin taro tare da hafsoshi da shugabanin gari. Da Festas ya ba da umarni, aka fito da Bulus wurinsu.
24 Fesadase amane sia: i, “Hina Agaliba amola dunu huluane guiguda: gilisi. Amo dunu ba: ma. Ema Yu fi dunu huluane guiguda: esala amola Yelusaleme moilai bai bagade ganodini esala, amo da ema halale fofada: sa. Ilia ha: giwane, e bogoma: ne medomusa: halasa.
Festas ya ce, “Sarki Agaribas da dukanku da kuke tare da mu a nan, kun ga mutumin nan, dukan Yahudawa sun gana da ni a Urushalima da nan kuma. Suna mani ihu cewa, bai chanchanta a bar shi da rai ba.
25 Be e da se imunusa: fofada: su amo defele wadela: le hamoi na da hamedafa ba: i. E da hisu Louma ouligisudafa ema fofada: musa: sia: i dagoiba: le, na da Louma gamane ouligisudafa ema asunasimusa: sia: i dagoi.
Na gane bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ba; amma saboda ya daukaka kara zuwa Kaisar, na yanke shawara in aika shi.
26 Be na da bai moloidafa Louma gamane ouligisudafa ema meloa dedene imunu gogoleiba: le, na da di ba: ma: ne amo dunu oule misi. Hina bagade Agaliba! Disu noga: le dawa: ma. Bai na da ema fofada: nanu, bai noga: i amo Louma gamane ouligisudafa ema dedemu hanai gala.
Amma ba ni da wani dalili na musamman da zan rubuta wasika ga Kaisar. Saboda wannan dalili na kawo shi gabanku, masamman kai ya sarki Agaribas. Domin in sami karin abin da zan rubuta game da shi.
27 E wadela: i hou mae ba: le, ema fofada: su noga: le hame dawa: le, udigili asunasimu da defea hame galebe.”
Gama a ganina wauta ce in aika dan sarka ba tare da na rubuta laifi a kansa ba.”

< Asunasi Dunu Ilia Hou 25 >