< Luuka 14 >

1 lulyahumile ikighono ikya Sabati. yeiluta kukaja ja jumo juno aale n'gooyo ghwa Vafalisayi kulia un'kate, vope vakale vivaanda pipi na pipi.
Wata ranar Asabaci, ya shiga gidan wani daya daga cikin shugabanin Farisawa domin cin abinci, mutane kuwa suna sa masa idanu.
2 pavulongolo pa mwene pwealyale umuunhu juno alyale ni nhaamu ja kufimba.
Sai ga wani a gabansa mai ciwon fara.
3 uYesu akavaposia avaagula ndaghilo isa vayahudi na vafarisayi. “ndaani, lunono kusosia umuunhu pakighono kya Sabaati, asi vuli?”
Yesu ya tambaye masanan attaura da Farisawa, “Ya halata a wakar a ranan Asabaci, ko a'a?”
4 neke avene vakava kimie, pe, uYesu akan'koola. akan'sosia na pikun'tavula alutaghe.
Amma suka yi shiru. Yesu kuwa ya kama shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi.
5 ghwope akavavuula akati,” ghweveni mukipugha kiinu juno ali nu mwana nambe ing'ombe jingaghwilile muliina ku kighono kya Sabati naikujisuuvula ng'hani ng'hani?”
Sai yace masu, “Wanene a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya fadi a rijiya ran Asabaci, ba zai fitar da shi nan da nan ba?”
6 aveene valyale vasila ngufu isakwamula ghano ghano vavaposisie.
Sai suka kasa ba da amsar wadannan abubuwa.
7 un'siki ghuno uYesu alyakagwile kwiti vala vano valyaghogholilue kwiti vasalwile ifitengo vwoghopua. avavula ikihwani akati, “
Sa'adda Yesu ya lura da yadda wadanda aka gayyato sun zabi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali yana ce masu,
8 ye mughongolua nu muunhu uya vutolani, nungikalaghe mufitengo fya vavaha. ulwakuva nukagwile kuti,
“Sa'adda wani ya gayyace ka zuwa bikin aure, kada ka zauna a wuri mai daraja, domin yana yiwuwa an gayyaci wani wanda ya fi ka daraja.
9 pano aghongolilue umuunhu juno ghwe mwoghopua kyongo kukila uve. un'siki ghughuo umuunhu juno avaghongolile
Sa'adda wanda ya gayyace ku duka biyu ya zo, zai ce maka, 'Ka ba mutumin nan wurinka,' sa'annan a kunyace za ka koma mazauni mafi kaskanci.
10 neke uve ungaghongolue, usalulaghe uvukalo vwa kuvusililo, kuvaanga neke kyande ikwiisa juno akungongolile ghwemwene atisaghe uve manyani, kila ghukale kuvulongolo. apuo ghuuva mwoghopua ku vano valipalikimo nuuve pamesa.
Amma idan an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi kaskanci, domin idan wanda ya gayyace ka ya zo, yana iya ce maka, 'Aboki, hawo nan mana'. Sannan za ka sami girma kenan a gaban dukan wadanda kuke zaune tare a kan teburi.
11 ulwakuva juno ikughinia uNguluve alyamwisia, juno ikujisia ghwe ighinisivua.
Duk wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, wanda ya kaskantar da kansa, kuma daukaka shi za a yi”.
12 Yesu kange akam'bula umuunhu juno umughongolile, 'pano ghukumpela ikyakulia kya pamwisi nambe ikya pakivwilile, ulekaghe pighongola avamanyani vaako nambe avanyalukolo vaako, nambe avanyakisina vaako, nambe avabading'hani vaako avamofu neke kwiiti avene valeke pikukughongola uve uhombe.
Yesu ya ce wa mutumin da ya gayyace shi, “Idan za ka gayyaci mutum cin abinci ko biki, kada ka gayyaci abokanka, ko 'yan'uwanka, ko danginka, ko makwabtanka masu arziki, kamar yadda suna iya gayyatar ka, sai ya zama an maida maka.
13 neke lino pano ghuvomba ikikulukulu, vaghongolaghe avamofu, avalema, na vavoofu,
Amma idan za ka kira biki sai ka gayyace matalauta, da nakasassu, da guragu, da makafi,
14 najuve ghufunyua, ulwakuva naviwesia kuhomba. ulwakuva ghuhombua muvusyukua vwa vanya kyang'haani.
za ka kuwa sami albarka da yake ba su da hanyar saka maka. Gama za a saka maka a ranar tashin masu adalci.”
15 un'siki huno jumonga mu vala vano vakikalile pamesa palikimo nu Yesu ati apulike aghuo, ghwope akavavula akati,” afunyilue jula juno ilia un'kate mu vutwa vwa Nguluve”.
Da daya daga cikin wadanda ke zama akan teburi da Yesu ya ji wadannan abubuwa, sai ya ce masa, “Albarka ta tabbata ga wanda zai ci abinci a mulkin Allah!”
16 neke uYesu akavavula akati,” umuunhu jumonga akavombile ikikulukulu ikikome, akaghongola avaanhu vinga,
Amma Yesu ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa.
17 un'siki ghuno ikikulukulu kifikile, akansung'ile um'bombi ghwake kukuvavula vano avaghongolilue, 'mwise, ulwakuva ifinu fyoni fivikilue tayale
Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa wadanda aka gayyata, “Ku zo, duk an shirya kome.”
18 vooni vakatengula kukunsuuma avasungukile ughwa kwanda akati 'nighulile umughunda nilonda nilute nikaghulole. sivuo usaghile,
Sai dukansu, suka fara kawo dalilai. Na farko ya ce masa, 'Na sayi gona, lalle ne in je in gan ta. Ina rokonka ka dauke mani.'
19 ghwope ujunga akati, 'nighulile ing'ombe ihaano najune nilute kughela. sivuo usaghile.
Sai wani ya ce, 'Na sayi shanu garma biyar, ina so in gwada su. Ina ronkan ka, ka dauke mani.'
20 na ju muunhu ujunge akati, 'nihumile pitoola un'dala pe lino naniwesia pikwisa.
Wani mutum kuma ya ce, 'Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.'
21 um'bombi akagomoka na kukum'bula um'baha ghwake aghuo. unyanyumba jula akakalile akam'bula um'bombi ghwake,' luta ng'hani ng'hani mumpulo na mufisila fino filuta mufikaaja fya vaanhu ukavalete apa avakotofu, avalema. vano navilola na vabofu”.
Da bawan ya zo ya fadi wa maigidansa wadannan abubuwa, sai maigidan yayi fushi, ya ce wa bawansa, jeka da sauri ka bi cikin titunan birni da kwararo-kwararo, ka kawo gajiyayyu, da nakasassu, da makafi, da guragu.'
22 um'bombi ghwake akati, ntwa aghuo ghano unilaghisie ghavombike, nambe lino ikyakulia kisighiile.
Sai bawan ya ce, 'Maigida, abin da ka umarta an gama, amma har yanzu da sauran wuri.”
23 untwa akam'bula um'bombi akati, luta kusila ijansevo na mufisila fino filuta mumakaaja gha vaanhu ukavapelepesie avaanhu vingile neke inyumba jango jimeme.
Sai maigidan ya ce wa bawan, 'Jeka, ka bi kwararo-kwararo da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana.
24 ulwakuva nikuvavula, mu vala vano vaghongolilue ulwa kwanda nakwale juno ilivonja ikikulukulu kyango.
Gama ina gaya maku, babu ko daya daga cikin mutanen da na gayyata da farko da zai dandana bikina.”
25 lino ulukong'ano ulukume valyale viluta naghwo. ghwope akadyetuka akavavula kuuti,
Ana nan, taron suna tafiya tare da shi, sai ya juya ya ce masu,
26 ndeve umuunhu ikwisa kulyune ghwope naikunkalalila ubaba ghwa ghwake, ungiina ghwake, avaanha vaake, avanyalukolo vaake avaghosi na vadala Ena, na vu vwumi vwake kange navuwesia kuva vavulanisivua vango.
“Duk mai zuwa wurina amma bai ki mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata ba - I, har da ransa ma, ba zai iya zama almajirina ba.
27 umuunhu nave naitoola ikikovekano kyake na kukwisa kunsana jango naiwesia kuva m'bulanisivua ghwango.
Duk wanda bai dauki gijiyensa ya biyo ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28 ulwakuva ghwe veni mu lyumue, juno ilonda kujenga kujenga aikela kutengula kiisatala iling'hanie taasi alole indalama neke alole kukughenia aghuo.
Wanene a cikinku wanda yake niyyar gina bene, da ba zai zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba tun da farko, ko yana da ishashen kudi da zai iya kare aikin?
29 nave naiovomba aghuo neke kyande ijenga uvwalo angakunue pimalisia. vooni vano vilola vitengula piseka,
Kada ya zama bayan da ya sa harsashin ginin, ya kasa gamawa, har duk wadanda suka gani su fara yi masa ba'a,
30 vitisagha, umuunhu uju akatengwile kujenga, akunilue kumalikisia.
su rika cewa, ga mutumin nan ya fara gini amma ya kasa gamawa.'
31 neke ghwe Ntwa muki, jno ilonda kuluta kutovana nu Ntwa ujunge mu vwiite, juno naikukala paasi taasi neke asaghe nave akwiline kutovana, palikimo na vaanhu imbilima kijigho kimo kutovana nu junge juno ikwisa kwa mwene na vaanhu imbilima fijigho fivili?
Ko kuwa wanne sarki ne, in za shi je yaki da wani sarki, da ba zai zauna da farko ya yi shawara ya ga ko shi mai jarumawa dubu goma zai iya karawa da dayan sarkin mai jarumawa dubu ashirin ba?
32 ndeve evuo ililugu lya vange pano lijighe lilikuvutali, likunsung'a untwa kusuuma ulwiho lya lutengano.
In kuwa ba zai iya ba, to tun wancan yana nesa, sai ya aiki wakili ya kuma tambayo sharudan salama.
33 kwekuti lino, juno nailonda kukufleka fyooni fino alinafyo. nangawesie kuva m'bulanisivua ghwango.
Haka ma, ba wani a cikinku wanda bai rabu da duk abin da ya mallaka ba, da zai iya zama almajirina.”
34 umwinyo nnono, neke nave ghunangike ghuvombela kiki neke ghuve mwinyo kange?
“Gishiri abu ne mai kyau, amma idan gishiri ya sane, da me za a dadada shi?
35 naghuva mwinyo ghwa kulunga nambe kuva mbolela. kange kutaghua kuvutali. umwene unya mbughulutu aghakupulika na apulikaghe”.
Ba shi da wani anfani a kasa, ko ya zama taki. Sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji.”

< Luuka 14 >