< 1 Petro 1 >

1 Petro, nsung'ua ghwa Yesu kilisite, kulyumue vabaghulivua, kuvasalulua, mu Pontoon joni, Galatia, Kapadokia, Asia ni Bithinia,
Bitrus, manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga zaɓaɓɓu na Allah, baƙi a duniya, da suke a warwatse ko’ina a Fontus, Galatiya, Kaffadokiya, Asiya da kuma Bitiniya,
2 kuhuma muvwelevua vwa Nguluve, Nhata, kuvalasivua nu Mhepo Mwimike, mulwa kumwoghopa u Yesu kiliste, na kuvalasivua vwimila idanda jaake. Uvumofu vuve numue, nu lutengano lwinu lwongelele.
waɗanda aka zaɓa bisa ga rigyasanin Allah Uba, ta wurin aikin tsarkakewar Ruhu, don biyayya ga Yesu Kiristi, su kuma sami yayyafan jininsa. Alheri da salama su zama naku a yalwace.
3 U Nguluve uNhaata ghwa Mutwa ghwitu Yesu kilisite aghinuaghe. Mulusungu ulwake uluvaha, alyatuholile vupia vwimila kukunsusia u Yesu kilisite kuhuma muva vufue,
Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi! Cikin jinƙansa mai girma ya ba mu sabuwar haihuwa cikin bege mai rai ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu,
4 kuuti twupile silo uNguluve alyalaghile kukuvapeela avanhu vaake avaviikile isio kukyanya kuno nasivola, nambe kunangika, nambe kusakala.
da kuma cikin gādon da ba zai taɓa lalacewa, ɓacewa ko koɗewa ba, ajiyayye a sama dominku,
5 Unguluve mungufu sake, ikuvalola vunofu vwimila ulwitiko lwinu kuvupoki vuno alig'hanisie kukuvahufia unsiki ughwa vusililo.
ku waɗanda ta wurin bangaskiya ake kiyayewa ta wurin ikon Allah har yă zuwa ceton da yake a shirye da za a bayyana a ƙarshen lokaci.
6 Muhovokaghe vwimila uluo, napanolino munoghile kusukunala vwimila ingelo sino silipapinga.
A kan wannan kuke cike da farin ciki ƙwarai, ko da yake yanzu na ɗan lokaci kuna fuskantar baƙin ciki daga gwaje-gwaje iri-iri.
7 Uluo, ulwakuva ulwitiko lwinulwinu luve mungelo, ulwitiko luno lunoghile kukila isahabu, jino jinangika mu mwoto ghuno ghughela ulwitiko lwinu, ulu luhumile kuuti ulwitiko lwinu luuve ulunyakupaala, ulunyakughinia, muvwoghopua mukighono ikya kugomoka u Yesu kilite.
Wannan kuwa domin a tabbatar da sahihancin bangaskiyarku ne, wadda ta fi zinariya daraja nesa, ita zinariya kuwa, ko da yake mai ƙarewa ce, akan gwada ta da wuta, domin bangaskiyan nan taku ta jawo muku yabo da girma da ɗaukaka a bayyanar Yesu Kiristi.
8 Umwene namumbwene, looli mumughanile. Namukumwagha lino, poope vwimila vwamwene muli nu lukeelo luno nalujoveka kulukelo luno lumemilue nu lughinio.
Ko da yake ba ku taɓa ganinsa ba, kuna ƙaunarsa; kuma ko da yake ba kwa ganinsa yanzu, kun gaskata shi, kun kuma cika da farin ciki ƙwarai, wanda ya fi gaban faɗi,
9 Vwimila ulwitiko lwinu lino mukwupila jumue, uvupoki vwa mojo ghinu.
gama kuna samun sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku ke nan.
10 Avavili vakalolesyagha fijo na vakaposelesia vakagule vule ilikuvapoka
Game da ceton nan, annabawa, waɗanda suka yi maganar alherin da za tă zo gare ku, sun yi bincike mai zurfi, a natse,
11 Ulwakuva uMhepo kilisite juno alyale mun'kate muveene, ilipumuka napambele iiva nu vuvaha. Valonda kuuti vakagule unsiki muki uMhepo wa kilisite juno alimun'kate muvanave alyale ijova keke navene. Ulu lulyahumile unsiki ghono alyale ikuvavula kuuti imumuko sa Kilisite nuvwimila vuno ngalivumbingilile.
suna ƙoƙari su san lokaci da kuma yanayin da Ruhun Kiristi da yake cikinsu yana nunawa sa’ad da ya yi faɗi a kan wahalolin Kiristi da kuma ɗaukaka da za tă bi.
12 Akavahufia avaviili kuuti imbombo jave ijakuvila najilyale vwimila aveene, loolilooli jilyale vwimila umue - imola isio musipulike kuhuma kuvaanhu vano vipulisia imola inofu mungufu isa Mhepo Mwimike Juno alyasung'hilu kuhuma kukyanya, imola isio avanyamola vinoghelua kukusikagula.
Aka bayyana musu cewa ba kansu ne suke bauta wa ba sai ku, sa’ad da suka yi maganar abubuwan da aka faɗa muku ta wurin waɗanda suka yi muku wa’azin bishara, ta wurin Ruhu Mai Tsarki wanda aka aika daga sama. Ko mala’iku ma suna marmari su ga waɗannan abubuwa.
13 Mu uluo muling'aniaghe kuluhala lwinhu. Muvesaghe nu lujisio mumasaghe ghinu. Mukangasiaghe na kuhuvila fijo ulusungu luno mulipelua ikighono kinno iligomoka.
Saboda haka, ku shirya kanku don aiki; ku zama masu kamunkai; ku kafa begenku duka a kan alherin da za a ba ku sa’ad da aka bayyana Yesu Kiristi.
14 Ndavule avaana avakundi, mulekaghe kulongosivua nuvunoghelua vwinu vuno mulyale navwo ye mukyale kukunkagula unguluve.
Kamar’ya’ya masu biyayya, kada ku bi mugayen sha’awace-sha’awacen da dā kuke da su sa’ad da kuke rayuwa a cikin jahilci.
15 Looli, muvisaghe vimike mumikalile agha vwumi vwinu vwoni, ndavule juno avakemelile vule mwimike.
Amma kamar yadda wanda ya kira ku yake mai tsarki, haka ku ma sai ku kasance masu tsarki cikin dukan abubuwan da kuke yi;
16 Ulwakuva lilembilue, “Muvesaghe vimike, ulwakuva une nilimwimike.”
gama a rubuce yake cewa, “Ku zama masu tsarki, domin ni mai tsarki ne.”
17 Kange ndave mukuntambula “Nhata” juno ikuvahigha avanhu vooni mumaghendele ghave, mujisiaghe nakuvingilila muvwumi vwinu vwoni
Tun da yake kuna kira ga Uba wanda yake yin wa kowane mutum shari’a bisa ga ayyukansa ba bambanci, sai ku yi rayuwarku a nan kamar baƙi cikin tsoro mai bangirma.
18 Mugagwile vule muvangilue kuhuma mumaghendele ghiinu ghano naghanoghile ghano mulyupile kuvakuulu viinu, nalyavavangile ni finu fino finangike ndavule indalama nambe isahabu.
Gama kun san cewa ba da abubuwa masu lalacewa kamar azurfa ko zinariya ce aka fanshe ku daga rayuwar banza da kuka karɓa daga kakanni-kakanninku ba,
19 Looli muvangilue ni danda inalamu ija Yesu kilisite, ndavule ija ng'holo ija litekelo, isila vulema nambe lideha.
sai dai an fanshe ku da jini mai daraja na Kiristi, ɗan rago marar aibi ko lahani.
20 Ukilisite alyasalulilue kuhuma m'bukuuku ye jikyale kupelua iisi, neke mumasiki agha aghavusililo, amuhofisie vwimila umue.
An zaɓe shi kafin halittar duniya, amma an bayyana shi a zamanin ƙarshe saboda ku.
21 Mukumwitika uNguluve vwimila umwene, juno u Nguluve alyansusisie kuhuma kuvafue nakumpeela uvuvaha kuuti mumwitikaghe na kukumuhuvila u Nguluve.
Ta gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya tā da shi daga matattu, aka kuma ɗaukaka shi, ta haka bari bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.
22 Muvalisie amoojo ghiinu vwimila kukunda uvwakyang'aani, nakukuvaghana avajinu kisila vukedusi, lino muvaghanaghe nu mwoojo ghwoni.
Yanzu da kuka tsarkake kanku ta wurin yin biyayya ga gaskiyan nan, don ku kasance da ƙauna mai gaskiya wa’yan’uwanku, sai ku ƙaunaci juna ƙwarai, daga zuciya.
23 Muholilue vupia, nakwekuti kuholua kim'bili ghuno ghufua ulwene muholilue kuuva nu vwumi uvusila kusila, mungufu isalisio lya Nguluve ilyafighono fyoni. (aiōn g165)
Gama an sāke haihuwarku, ba da iri da yake lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, ta wurin rayayyiya da kuma madawwamiyar maganar Allah. (aiōn g165)
24 Ulwakuva “Amavili ghooni ghalindavule ilisoli, utogo lwake lwoni lulindavule ililuva lya lisoli. ilisoli linyala, ililuva lijoghotoka nakusanguka,
Gama, “Dukan mutane kamar ciyawa suke, darajarsu kuma kamar furannin jeji ne; ciyawa takan yanƙwane furannin kuma su kakkaɓe,
25 looli ilisio lya Nguluve lijigha kisila kusila lusiku.” Ili lye lisio lino je mola jino jipulisivue kulyumue. (aiōn g165)
amma maganar Ubangiji tana nan har abada.” Wannan kuwa ita ce kalmar da aka yi muku wa’azi. (aiōn g165)

< 1 Petro 1 >